< Firistoci 7 >

1 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodi na hadaya don laifi, hadaya ce tsattsarka.
This also is the law of the sacrifice for a trespass, it is most holy:
2 Za a yanka hadaya don laifi a inda ake yanka hadaya ta ƙonawa, za a kuma yayyafa jinin a kowane gefe na bagade.
Therefore where the holocaust is immolated, the victim also for a trespass shall be slain: the blood thereof shall be poured round about the altar.
3 Za a miƙa kitsen abin hadaya duka, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki,
They shall offer thereof the rump and the fat that covereth the entrails:
4 da ƙodoji biyu da kitsen da yake a bisansu kusa da kwiɓi, da kuma rufin hanta, wanda za a cire tare da ƙodoji.
The two little kidneys, and the fat which is by the flanks, and the caul of the liver with the little kidneys.
5 Firist zai ƙone su a kan bagade, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce don laifi.
And the priest shall burn them upon the altar: it is the burnt sacrifice of the Lord for a trespass.
6 Kowane da namiji cikin iyalin firistoci zai iya ci. Sai a tsattsarkan wuri ne za a ci; gama abu mafi tsarki ne.
Every male of the priestly race, shall eat this flesh in a holy place, because it is most holy.
7 “‘Hadaya don laifi kamar hadaya don zunubi take, saboda haka ƙa’ida hanyar yinsu iri ɗaya ce. Su ɗin na firist da ya yi kafara da su ne.
As the sacrifice for sin is offered, so is also that for a trespass: the same shall be the law of both these sacrifices: it shall belong to the priest that offereth it.
8 Firist da ya miƙa hadaya ta ƙonawa domin wani, zai iya ajiye fatar wa kansa.
The priest that offereth the victim of holocaust, shall have the skin thereof.
9 Kowace hadaya ta garin da aka toya a tanda, ko aka dafa a tukunya ko a kan kaskon tuya, na firist da ya miƙa ta ne,
And every sacrifice of flour that is baked in the oven, and whatsoever is dressed on the gridiron, or in the fryingpan, shall be the priest’s that offereth it:
10 kuma kowace hadaya ta gari wadda aka kwaɓa da mai, ko wadda ba a kwaɓa ba, ita ma, ta dukan’ya’ya Haruna ne maza.
Whether they be tempered with oil, or dry, all the sons of Aaron shall have one as much as another.
11 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodin hadaya don zumuncin da mutum zai iya miƙa ga Ubangiji.
This is the law of the sacrifice of peace offerings that is offered to the Lord.
12 “‘In ya miƙa hadayar a matsayin hadaya ta godiya ce, to, zai miƙa ta tare da burodi mai kauri marar yisti, wanda aka kwaɓa da mai, da burodi marar kauri, wanda aka shafa wa mai, da kuma burodi mai kauri da aka yi da gari mai laushi wanda aka kwaɓa sosai da mai.
If the oblation be for thanksgiving, they shall offer leaves without leaven tempered with oil, and unleavened wafers anointed with oil, and fine flour fried, and cakes tempered and mingled with oil:
13 Tare da hadayarsa don zumunci ta godiya, zai miƙa dunƙulen burodin da aka yi da yisti.
Moreover leaves of leavened bread with the sacrifice of thanks, which is offered for peace offerings:
14 Zai kuma kawo ɗaya daga kowace a matsayin hadaya, baiko ne ga Ubangiji. Wannan zai zama na firist da ya yafa jinin hadaya ta salama ne.
Of which one shall be offered to the Lord for firstfruits, and shall be the priest’s that shall pour out the blood of the victim.
15 Za a ci wannan nama na hadaya don zumunci ta godiya a ranar da aka miƙa ta, kada yă bar wani abu daga naman yă kwana.
And the flesh of it shall be eaten the same day, neither shall any of it remain until the morning.
16 “‘In hadayarsa cika wa’adin rantsuwa ce ko kuwa ta yardar rai ce, sai a ci hadayar a ranar da ya miƙa ta, amma za a iya cin duk abin da ya rage kashegari.
If any man by vow, or of his own accord offer a sacrifice, it shall in like manner be eaten the same day: and if any of it remain until the morrow, it is lawful to eat it:
17 Duk naman hadayar da ya rage har kwana uku, dole a ƙone shi.
But whatsoever shall be found on the third day shall be consumed with fire.
18 Idan aka ci naman hadayarsa ta salama a rana ta uku, ba za a karɓi wanda ya ba da hadayar har ya sami albarkar hadayar ba, naman zai zama abin ƙyama, duk wanda ya ci kuwa ya yi laifi.
If any man eat of the flesh of the victim of peace offerings on the third day, the oblation shall be of no effect, neither shall it profit the offerer: yea rather whatsoever soul shall defile itself with such meat, shall be guilty of transgression.
19 “‘Ba za a ci naman da ya taɓa wani abu marar tsarki ba; dole a ƙone shi. Game da sauran nama, kowa da yake mai tsarki zai iya ci.
The flesh that hath touched any unclean thing, shall not be eaten, but shall be burnt with fire: he that is clean shall eat of it.
20 Amma in wani wanda ba shi da tsarki ya ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
If any one that is defiled shall eat of the flesh of the sacrifice of peace offerings, which is offered to the Lord, he shall be cut off from his people.
21 Idan wani mutum ya taɓa abu marar tsarki, ko mutum ne, ko dabba ce, ko wani abu na banƙyama, ya kuma ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a fid da mutumin daga cikin mutanensa.’”
And he that hath touched the uncleanness of man, or of beast, or of any thing that can defile, and shall eat of such kind of flesh, shall be cut off from his people.
22 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
23 “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Kada ku ci wani kitsen shanu, ko na tumaki, ko kuwa na awaki.
Say to the children of Israel: The fat of a sheep, and of an ox, and of a goat you shall not eat.
24 Za a iya yin wani amfani da kitsen dabbar da ta mutu mushe, ko kitsen dabbar da namun jeji su yayyaga, amma kada a kuskura a ci.
The fat of a carcass that hath died of itself, and of a beast that was caught by another beast, you shall have for divers uses.
25 Duk wanda ya ci kitsen dabbar da aka miƙa ta wuta ga Ubangiji, za a fid da shi daga mutanensa.
If any man eat the fat that should be offered for the burnt sacrifice of the Lord, he shall perish out of his people.
26 Kuma duk inda kuke zama, ba za ku ci jinin wani tsuntsu ko na dabba ba.
Moreover you shall not eat the blood of any creature whatsoever, whether of birds or beasts.
27 Duk wanda ya ci jini, za a fid da mutumin daga mutanensa.’”
Every one that eateth blood, shall perish from among the people.
28 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
29 “Faɗa wa Isra’ilawa, ‘Duk wanda ya kawo hadaya ta salama ga Ubangiji, sai ya kawo hadayarsa ga Ubangiji daga cikin hadayu na salama.
Speak to the children of Israel, saying: He that offereth a victim of peace offerings to the Lord, let him offer therewith a sacrifice also, that is, the libations thereof.
30 Da hannuwansa zai kawo hadayar da za a ƙona ga Ubangiji; zai kawo kitsen tare da ƙirjin, yă kuma kaɗa ƙirjin a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa.
He shall hold in his hands the fat of the victim, and the breast: and when he hath offered and consecrated both to the Lord, he shall deliver them to the priest,
31 Firist zai ƙone kitsen a bisa bagade, amma ƙirjin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza.
Who shall burn the fat upon the altar, but the breast shall be Aaron’s and his sons’.
32 Za ku ba da cinya ta dama ta hadaya don zumuncinku ga firist a matsayin baiko.
The right shoulder also of the victims of peace offerings shall fall to the priest for firstfruits.
33 Ɗan Haruna da ya miƙa jini da kitsen hadaya ta salama, zai ɗauki cinyar tă zama rabonsa.
He among the sons of Aaron, that offereth the blood, and the fat, he shall have the right shoulder also for his portion.
34 Daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa, na ɗauki ƙirjin da aka kaɗa da kuma cinyar da aka miƙa, na ba da su ga Haruna firist da kuma’ya’yansa maza a matsayin rabonsu na kullum daga Isra’ilawa.’”
For the breast that is elevated and the shoulder that is separated I have taken of the children of Israel, from off their victims of peace offerings, and have given them to Aaron the priest, and to his sons, by a law for ever, from all the people of Israel.
35 Wannan shi ne sashen hadayar da aka ba wa Haruna da’ya’yansa maza, hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta, tun ranar da aka gabatar da su don su yi wa Ubangiji hidima a matsayin firist.
This is the anointing of Aaron and his sons, in the ceremonies of the Lord, in the day when Moses offered them, that they might do the office of priesthood,
36 A ranar da aka keɓe su, Ubangiji ya umarta cewa Isra’ilawa su ba da wannan a gare su a matsayin rabonsu na kullum, a dukan tsararraki masu zuwa.
And the things that the Lord commanded to be given them by the children of Israel, by a perpetual observance in their generations.
37 Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, hadaya don zunubi, hadaya don laifi, hadaya ta naɗi da kuma hadaya ta salama,
This is the law of holocaust, and of the sacrifice for sin, and for trespass, and for consecration, and the victims of peace offerings:
38 waɗanda Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai, a Hamadar Sinai, a ranar da ya umarci Isra’ilawa su kawo hadayunsu ga Ubangiji.
Which the Lord appointed to Moses in mount Sinai, when he commanded the children of Israel, that they should offer their oblations to the Lord in the desert of Sinai.

< Firistoci 7 >