< Firistoci 6 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
2 “In wani ya yi zunubi bai kuma yi aminci ga Ubangiji ba, wato, ta wurin yin wa abokin zamansa karya game da ajiyar da abokin ya ba shi amana, ko a kan wani alkawarin da suka yi wa juna, ko kuwa a kan yă cuci abokin,
»Če duša greši in zagreši prekršek zoper Gospoda in laže svojemu bližnjemu v tem, kar mu je bilo izročeno, da varuje, ali v družbi, ali v stvari, odvzeti z nasiljem, ali je zavedel svojega bližnjega,
3 ko kuma idan ya sami abin da ya ɓace amma ya yi ƙarya cewa bai samu ba. Ko ya yi rantsuwar ƙarya a kan duk irin abubuwan da akan aikata na laifi,
ali je našel to, kar je bilo izgubljeno in glede tega laže in krivo prisega; v čemerkoli izmed vsega tega kar človek dela, v tem greši;
4 sa’ad da mutum ya yi irin laifin nan, ya kuwa tabbata mai laifi ne, to, sai yă komar da abin da ya ƙwace, ko abin da ya samu ta hanyar zalunci, ko abin da aka ba shi ajiya, ko abin da ya tsinta.
Potem se bo zgodilo, ker je grešil in je kriv, da bo povrnil to, kar je nasilno odvzel proč ali stvar, ki jo je varljivo pridobil ali to, kar mu je bilo izročeno, da varuje ali izgubljeno stvar, ki jo je našel,
5 Zai mai da abin da ya yi rantsuwar ƙarya a kai. Zai mayar wa mai abin da abinsa a yadda yake, har yă ƙara kashi ashirin bisa ɗari na abin. A ranar da zai yi hadaya don laifinsa, a ranar ce zai mayar wa mai abin da abinsa.
ali vse to o čemer je krivo prisegel. To bo torej povrnil v glavnici in k temu bo dodal še petino in to dal tistemu, ki mu pripada, na dan svoje daritve za prekršek.
6 A matsayin hakki kuwa, dole yă kawo wa firist, wato, ga Ubangiji, hadaya rago marar lahani kuma wanda aka kimanta tamaninsa daga garke don laifinsa.
H Gospodu bo [prek] duhovnika privedel svojo daritev za prestopek, ovna brez pomanjkljivosti iz tropa, s tvojo oceno, v daritev za prestopek.
7 Ta haka firist zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji, za a kuwa gafarta masa irin laifin da ya yi.”
Duhovnik bo zanj pred Gospodom opravil spravo in odpuščeno mu bo za karkoli od vsega, kar je storil v teh prekrških.«
8 Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
9 “Ka ba Haruna da’ya’yansa maza wannan umarni, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa. Hadaya ta ƙonawa za tă kasance a bagade dukan dare, sai da safe, kuma dole a bar wutar tă yi ta ci a bisa bagaden.
»Zapovej Aronu in njegovim sinovom, rekoč: ›To je postava žgalne daritve: ›To je žgalna daritev, ker vso noč, do jutra, gori na oltarju in oltarni ogenj bo gorel v njej.‹
10 Sa’an nan firist zai sa rigunarsa ta lilin da kuma rigar lilin da ake sa a ciki, sa’an nan yă kwashe tokan hadaya ta ƙonawa da wuta da ta ci a kan bagaden, yă sa kusa da bagaden.
Duhovnik si bo nadel laneno obleko in kratke platnene hlače bo nadel na svoje meso in pobral pepel, ki ga je ogenj na oltarju použil z žgalno daritvijo in ga položil poleg oltarja.
11 Sa’an nan yă tuɓe waɗannan rigunan yă sa waɗansu, sa’an nan yă ɗauki tokar yă kai waje da sansani zuwa inda yake da tsabta.
Odložil bo svoje obleke in si nadel druge obleke in pepel odnesel zunaj tabora, na čist prostor.
12 Dole a bar wutar da take bisa bagaden tă yi ta ci; kada tă mutu. Kowace safiya firist zai ƙara itacen wuta, yă shirya hadaya ta ƙonawa a bisa wutar yă kuma ƙone kitsen hadaya ta salama a kansa.
Ogenj na oltarju naj gori na njem; naj ne bo ugasnjen. Duhovnik naj na njem vsako jutro zažiga les in nanj po vrsti polaga žgalno daritev in na njem naj zažiga tolščo mirovnih daritev.
13 Dole a bar wutar tă ci gaba da ci a bisa bagade; kada tă mutu.
Ogenj bo vedno gorel na oltarju; nikoli naj ne ugasne.
14 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya ta gari.’Ya’yan Haruna za su kawo ta a gaban Ubangiji, a gaban bagaden.
To je postava jedilne daritve. Aronovi sinovi jo bodo darovali pred Gospodom, pred oltarjem.
15 Firist zai ɗiba garin hadayar mai laushin wanda aka zuba masa mai da kuma turare cike da tafin hannu. Zai ƙona wannan a bisa bagaden, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji don tunawa.
Od tega bo vzel prgišče moke jedilne daritve in od olja in vse kadilo, ki je na jedilni daritvi in to bo na oltarju sežgal Gospodu v prijeten vonj, torej spomin na to.
16 Haruna da’ya’yansa maza za su ci sauran, amma za a ci shi ba tare da yisti ba a tsattsarkan wuri; za su ci shi a harabar Tentin Sujada.
Preostanek pa bodo Aron in njegovi sinovi pojedli. Z nekvašenim kruhom bo pojedena na svetem prostoru. Na dvoru šotorskega svetišča skupnosti jo bodo pojedli.
17 Ba za a toya shi da yisti ba; na ba su yă zama rabonsu daga cikin hadayun da ake ƙonawa da wuta, abu ne mafi tsarki, kamar hadaya don zunubi da laifi.
Ta ne bo pečena s kvasom. To sem jim dal za njihov delež mojih daritev, narejenih z ognjem; to je najsvetejše, kakor je daritev za greh in kakor daritev [za] prekršek.
18 Kowane ɗa namiji cikin zuriyar Haruna zai iya cinsa. Wannan rabonsa ne na kullum na hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta. Wannan madawwamiyar doka ce cikin zamananku duka. Duk abin da ya taɓa hadayun zai tsarkaka.’”
Vsi moški izmed Aronovih otrok bodo jedli od nje. To bo zakon na veke v vaših rodovih glede Gospodovih daritev, narejenih z ognjem; vsak, kdor se jih dotakne, bo svet.‹«
19 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
20 “Wannan ne hadayar da Haruna da’ya’yansa maza za su kawo ga Ubangiji a ranar da za a naɗa su firistoci, humushin garwan gari mai laushi a matsayin hadaya ta gari na kullum, rabinsa da safe, rabinsa kuma da yamma.
»To je dar Arona in njegovih sinov, ki ga bodo darovali Gospodu na dan, ko je maziljen: deseti del škafa fine moke za neprestano jedilno daritev, polovico od tega zjutraj in polovico od tega zvečer.
21 A shirya shi da mai a kwanon tuya, a kawo shi kwaɓaɓɓe sosai, a miƙa shi hadaya ta gari dunƙule-dunƙule don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
V ponvi naj bo pripravljena z oljem in ko je ocvrta, jo boš v njej prinesel in pečene koščke jedilne daritve boš daroval v prijeten vonj Gospodu.
22 Duk wanda aka naɗa daga’ya’yan Haruna yă zama firist a madadinsa, shi ne zai miƙa wannan hadayar ga Ubangiji. Zai ƙone hadayar ƙurmus. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce har abada.
To naj daruje duhovnik izmed njegovih sinov, ki je maziljen namesto njega. To je zakon na veke Gospodu; ta naj bo v celoti sežgana.
23 Kowace hadaya ta gari ta firist, za a ƙone ta ƙurmus, ba za a ci ba.”
Kajti vsaka jedilna daritev za duhovnika naj bo v celoti sežgana. Le-ta naj ne bo pojedena.«
24 Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
25 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya don zunubi. Za a yanka hadaya don zunubi a gaban Ubangiji a inda ake yankan hadaya ta ƙonawa; dole tă kasance mai tsarki.
»Govori Aronu in njegovim sinovom, rekoč: ›To je postava daritve za greh pred Gospodom. Na kraju, kjer je zaklana žgalna daritev, bo zaklana daritev za greh. To je najsvetejše.
26 Firist da ya miƙa ta zai ci, za a ci ta a tsattsarkan wuri, a harabar Tentin Sujada.
Jedel jo bo duhovnik, ki jo daruje za greh. Pojedena bo na svetem kraju, na dvoru šotorskega svetišča skupnosti.
27 Duk abin da ya taɓa wani sashe na naman, zai zama da tsarki, kuma in wani jini ya ɗiga a riga, dole ka wanke shi a tsattsarkan wuri.
Karkoli od tega se bo dotaknilo mesa, naj bo sveto, in ko je kri od te daritve poškropljena na kakršnokoli obleko, boš na svetem prostoru opral to, po čemer je bila poškropljena.
28 Dole a farfashe tukunyar lakar da aka dafa naman a ciki; amma in an dafa a tukunyar tagulla, sai a kankare tukunyar, a kuma ɗauraye da ruwa.
Toda lončena posoda, v kateri je skuhana, naj bo razbita, in če je skuhana v bronastem loncu, naj bo tako odrgnjena kakor pomita v vodi.
29 Kowane namiji a iyalin firistoci zai iya ci; gama abu ne mafi tsarki.
Vsi moški izmed duhovnikov bodo jedli od tega. To je najsvetejše.
30 Amma duk wata hadaya don zunubi wadda aka kawo jininta cikin Tentin Sujada don a yi kafara a Wuri Mai Tsarki, ba za a ci ba. A maimako haka za a ƙone ta ɗungum.
Nobena daritev za greh, od katere je kakršnakoli kri prinesena v šotorsko svetišče skupnosti, da se z njo pobota na svetem kraju, naj ne bo pojedena. Ta naj bo sežgana v ognju.