< Firistoci 6 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spake vnto Moses, saying,
2 “In wani ya yi zunubi bai kuma yi aminci ga Ubangiji ba, wato, ta wurin yin wa abokin zamansa karya game da ajiyar da abokin ya ba shi amana, ko a kan wani alkawarin da suka yi wa juna, ko kuwa a kan yă cuci abokin,
If any sinne and commit a trespasse against the Lord, and denie vnto his neighbour that, which was take him to keepe, or that which was put to him of trust, or doth by robberie, or by violence oppresse his neighbour,
3 ko kuma idan ya sami abin da ya ɓace amma ya yi ƙarya cewa bai samu ba. Ko ya yi rantsuwar ƙarya a kan duk irin abubuwan da akan aikata na laifi,
Or hath found that which was lost, and denieth it, and sweareth falsely, for any of these things that a man doeth, wherein he sinneth:
4 sa’ad da mutum ya yi irin laifin nan, ya kuwa tabbata mai laifi ne, to, sai yă komar da abin da ya ƙwace, ko abin da ya samu ta hanyar zalunci, ko abin da aka ba shi ajiya, ko abin da ya tsinta.
When, I say, he thus sinneth and trespasseth, he shall then restore the robbery that he robbed, or the thing taken by violence which hee tooke by force, or the thing which was deliuered him to keepe, or the lost thing which he founde,
5 Zai mai da abin da ya yi rantsuwar ƙarya a kai. Zai mayar wa mai abin da abinsa a yadda yake, har yă ƙara kashi ashirin bisa ɗari na abin. A ranar da zai yi hadaya don laifinsa, a ranar ce zai mayar wa mai abin da abinsa.
Or for whatsoeuer he hath sworne falsely, he shall both restore it in the whole summe, and shall adde the fift parte more thereto, and giue it vnto him to whome perteyneth, the same day that he offreth for trespasse.
6 A matsayin hakki kuwa, dole yă kawo wa firist, wato, ga Ubangiji, hadaya rago marar lahani kuma wanda aka kimanta tamaninsa daga garke don laifinsa.
Also he shall bring for his trespasse vnto the Lord, a ramme without blemish out of the flocke in thy estimation worth two shekels for a trespasse offring vnto the Priest.
7 Ta haka firist zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji, za a kuwa gafarta masa irin laifin da ya yi.”
And the Priest shall make an atonement for him before the Lord, and it shall be forgiuen him, whatsoeuer thing he hath done, and trespassed therein.
8 Ubangiji ya ce wa Musa,
Then the Lord spake vnto Moses, saying,
9 “Ka ba Haruna da’ya’yansa maza wannan umarni, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi don hadaya ta ƙonawa. Hadaya ta ƙonawa za tă kasance a bagade dukan dare, sai da safe, kuma dole a bar wutar tă yi ta ci a bisa bagaden.
Commaund Aaron and his sonnes, saying, This is the lawe of the burnt offring, (it is the burnt offring because it burneth vpon the altar al the night vnto the morning, and the fire burneth on the altar)
10 Sa’an nan firist zai sa rigunarsa ta lilin da kuma rigar lilin da ake sa a ciki, sa’an nan yă kwashe tokan hadaya ta ƙonawa da wuta da ta ci a kan bagaden, yă sa kusa da bagaden.
And the Priest shall put on his linen garment, and shall put on his linen breeches vpon his flesh, and take away the ashes when the fire hath consumed the burnt offring vpon the altar, and he shall put them beside the altar.
11 Sa’an nan yă tuɓe waɗannan rigunan yă sa waɗansu, sa’an nan yă ɗauki tokar yă kai waje da sansani zuwa inda yake da tsabta.
After, he shall put off his garments, and put on other raiment, and cary the ashes foorth without the hoste vnto a cleane place.
12 Dole a bar wutar da take bisa bagaden tă yi ta ci; kada tă mutu. Kowace safiya firist zai ƙara itacen wuta, yă shirya hadaya ta ƙonawa a bisa wutar yă kuma ƙone kitsen hadaya ta salama a kansa.
But the fire vpon the altar shall burne thereon and neuer be put out: wherefore the Priest shall burne wood on it euery morning, and lay the burnt offering in order vpon it, and he shall burne thereon the fat of the peace offrings.
13 Dole a bar wutar tă ci gaba da ci a bisa bagade; kada tă mutu.
The fire shall euer burne vpon the altar, and neuer go out.
14 “‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya ta gari.’Ya’yan Haruna za su kawo ta a gaban Ubangiji, a gaban bagaden.
Also this is the lawe of the meate offring, which Aarons sonnes shall offer in the presence of the Lord, before the altar.
15 Firist zai ɗiba garin hadayar mai laushin wanda aka zuba masa mai da kuma turare cike da tafin hannu. Zai ƙona wannan a bisa bagaden, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji don tunawa.
He shall euen take thence his handfull of fine flowre of the meate offring and of the oyle, and all the incense which is vpon the meat offring, and shall burne it vpon the altar for a sweete sauour, as a memoriall therefore vnto the Lord:
16 Haruna da’ya’yansa maza za su ci sauran, amma za a ci shi ba tare da yisti ba a tsattsarkan wuri; za su ci shi a harabar Tentin Sujada.
But the rest thereof shall Aaron and his sonnes eate: it shalbe eaten without leauen in the holy place: in the court of the Tabernacle of the Congregation they shall eate it.
17 Ba za a toya shi da yisti ba; na ba su yă zama rabonsu daga cikin hadayun da ake ƙonawa da wuta, abu ne mafi tsarki, kamar hadaya don zunubi da laifi.
It shall not be baken with leauen: I haue giuen it for their portion of mine offrings made by fire: for it is as the sinne offering and as the trespasse offring.
18 Kowane ɗa namiji cikin zuriyar Haruna zai iya cinsa. Wannan rabonsa ne na kullum na hadayar da aka yi ga Ubangiji da wuta. Wannan madawwamiyar doka ce cikin zamananku duka. Duk abin da ya taɓa hadayun zai tsarkaka.’”
All the males among the children of Aaron shall eate of it: It shalbe a statute for euer in your generations concerning the offrings of the Lord, made by fire: whatsoeuer toucheth them shall be holy.
19 Ubangiji ya kuma ce wa Musa,
Agayne the Lord spake vnto Moses, saying,
20 “Wannan ne hadayar da Haruna da’ya’yansa maza za su kawo ga Ubangiji a ranar da za a naɗa su firistoci, humushin garwan gari mai laushi a matsayin hadaya ta gari na kullum, rabinsa da safe, rabinsa kuma da yamma.
This is the offering of Aaron and his sonnes, which they shall offer vnto the Lord in the day when he is anointed: the tenth part of an Ephah of fine floure, for a meate offering perpetuall: halfe of it in ye morning, and halfe thereof at night.
21 A shirya shi da mai a kwanon tuya, a kawo shi kwaɓaɓɓe sosai, a miƙa shi hadaya ta gari dunƙule-dunƙule don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
In the frying panne it shalbe made with oyle: thou shalt bring it fryed, and shalt offer the baken pieces of the meate offering for a sweete sauour vnto the Lord.
22 Duk wanda aka naɗa daga’ya’yan Haruna yă zama firist a madadinsa, shi ne zai miƙa wannan hadayar ga Ubangiji. Zai ƙone hadayar ƙurmus. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce har abada.
And the Priest that is anointed in his steade, among his sonnes shall offer it: It is the Lordes ordinance for euer, it shall be burnt altogether.
23 Kowace hadaya ta gari ta firist, za a ƙone ta ƙurmus, ba za a ci ba.”
For euery meate offring of the Priest shall be burnt altogether, it shall not be eaten.
24 Ubangiji ya ce wa Musa,
Furthermore, the Lord spake vnto Moses, saying,
25 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, ‘Waɗannan su ne ƙa’idodi domin hadaya don zunubi. Za a yanka hadaya don zunubi a gaban Ubangiji a inda ake yankan hadaya ta ƙonawa; dole tă kasance mai tsarki.
Speake vnto Aaron, and vnto his sonnes, and say, This is the Lawe of the sinne offering, In the place where the burnt offring is killed, shall the sinne offring be killed before the Lord, for it is most holy.
26 Firist da ya miƙa ta zai ci, za a ci ta a tsattsarkan wuri, a harabar Tentin Sujada.
The Priest that offreth this sinne offring, shall eate it: in the holy place shall it be eaten, in the court of ye Tabernacle of the Congregation.
27 Duk abin da ya taɓa wani sashe na naman, zai zama da tsarki, kuma in wani jini ya ɗiga a riga, dole ka wanke shi a tsattsarkan wuri.
Whatsoeuer shall touch the flesh thereof shalbe holy: and when there droppeth of the blood thereof vpon a garment, thou shalt wash that whereon it droppeth in the holy place.
28 Dole a farfashe tukunyar lakar da aka dafa naman a ciki; amma in an dafa a tukunyar tagulla, sai a kankare tukunyar, a kuma ɗauraye da ruwa.
Also the earthen pot that it is sodden in, shalbe broken, but if it be sodden in a brasen pot, it shall both be scoured and washed with water.
29 Kowane namiji a iyalin firistoci zai iya ci; gama abu ne mafi tsarki.
All the males among the Priestes shall eate thereof, for it is most holy.
30 Amma duk wata hadaya don zunubi wadda aka kawo jininta cikin Tentin Sujada don a yi kafara a Wuri Mai Tsarki, ba za a ci ba. A maimako haka za a ƙone ta ɗungum.
But no sinne offering, whose blood is brought into the Tabernacle of the Congregation to make reconciliation in the holy place, shalbe eaten, but shalbe burnt in the fire.

< Firistoci 6 >