< Firistoci 5 >
1 “‘Mutum zai yi zunubi in bai yi magana ba sa’ad da ya ji ana shelar neman shaida game da wani abin da ya gani ko kuwa ya ji, alhakin zai zauna a wuyansa.
And if a soul sins, in that he hears the voice of an oath, he being a witness, whether he has seen or known, if he does not testify, then he shall bear his iniquity.
2 “‘Ko kuwa in mutum ya taɓa wani abin da yake mai ƙazanta, ko gawar naman jeji marar tsabta, ko na shanu marar tsabta, ko na halittu marasa tsabtan da suke motsi a ƙasa; ko da yake bai sani ba, ya ƙazantu ke nan, kuma ya yi laifi.
Or if a soul touches any unclean thing, whether it be the carcass of an unclean beast, or the carcass of unclean cattle, or the carcass of unclean creeping things, and it be hidden from him, and he be unclean, then he shall be guilty.
3 Ko kuwa in ya taɓa rashin tsabta na mutane, wani abin da zai sa shi rashin tsabta; ko da yake bai sani ba, sa’ad da ya gane, zai zama mai laifi.
Or if he touch the uncleanness of man, whatever his uncleanness be with which he is unclean, and it be hid from him, when he knows of it, then he shall be guilty.
4 Ko kuwa in mutum bai yi tunani ba, ya yi rantsuwar yin wani abu, ko mai kyau ko marar kyau; ko da yake bai sani ba, duk da haka sa’ad da ya gane zai zama mai laifi.
Or if a soul swears rashly with his lips to do evil, or to do good, whatever it be that a man shall utter rashly with an oath, and it be hid from him, when he realizes it, then he shall be guilty in one of these.
5 Sa’ad da wani yana da laifi a kowanne cikin waɗannan hanyoyi, dole yă furta a hanyar da ya yi zunubin
And it shall be, when he shall be guilty in one of these, that he shall confess that by which he has sinned.
6 kuma don zunubin da ya yi, dole yă kawo wa Ubangiji tunkiya ko akuya daga garke kamar hadaya don zunubi; firist kuwa zai yi kafara dominsa da kuma domin zunubinsa.
And he shall bring his trespass offering to Jehovah for his sin which he has sinned, a female from the flock, a lamb or a goat, for a sin offering. And the priest shall make atonement for him as concerning his sin.
7 “‘In ba zai iya kawo tunkiyar ba, sai yă kawo kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu ga Ubangiji a matsayin hakki don zunubinsa, ɗaya domin hadaya don zunubi ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa.
And if his means is not sufficient for a lamb, then he shall bring his trespass offering for that by which he has sinned, two turtle-doves, or two young pigeons, to Jehovah, one for a sin offering, and the other for a burnt offering.
8 Zai kawo su wa firist, wanda da fari zai miƙa ɗaya domin hadaya don zunubi. Zai murɗe kan daga wuyanta, ba tare da tsinke kan gaba ɗaya ba,
And he shall bring them to the priest, who shall offer that which is for the sin offering first, and wring off its head from its neck, but shall not divide it apart.
9 zai kuma yayyafa jinin hadaya don zunubin a gefen bagade; a tsiyaye sauran jinin kuma a gindin bagade. Hadaya ce ta zunubi.
And he shall sprinkle of the blood of the sin offering upon the side of the altar, and the rest of the blood shall be drained out at the base of the altar. It is a sin offering.
10 Firist zai miƙa ɗayan matsayin hadaya ta ƙonawa bisa ga yadda aka tsara, yă kuma yi kafara dominsa saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta masa.
And he shall offer the second for a burnt offering, according to the ordinance. And the priest shall make atonement for him as concerning his sin which he has sinned, and he shall be forgiven.
11 “‘In ba zai iya kawo kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu ba, sai yă kawo humushin garwan gari mai laushi domin hadaya don zunubi. Ba lalle ba ne yă sa mai ko turare a kansa, saboda wannan hadaya ce ta zunubi.
But if his means is not sufficient for two turtle-doves, or two young pigeons, then he shall bring his oblation for that by which he has sinned, the tenth part of an ephah of fine flour for a sin offering. He shall put no oil upon it, nor shall he put any frankincense on it, for it is a sin offering.
12 Zai kawo wa firist, firist kuwa zai ɗiba da hannu don yă kasance abin tunawa, sai yă ƙone a bisan bagaden kamar hadayar da ake ƙona da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce ta zunubi.
And he shall bring it to the priest, and the priest shall take his handful of it as the memorial of it, and burn it on the altar, upon the offerings of Jehovah made by fire. It is a sin offering.
13 Ta haka firist zai yi kafara dominsa saboda dukan waɗannan zunuban da ya yi, za a kuwa gafarta masa. Sauran hadayar za tă zama ta firist, kamar yadda yake bisa ga hadaya ta gari.’”
And the priest shall make atonement for him concerning his sin that he has sinned in any of these things, and he shall be forgiven. And the remnant shall be the priest's, as the meal offering.
14 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
15 “Sa’ad da mutum ya ci amana, ya kuma yi zunubi ba da gangan ba dangane da wani cikin abubuwa masu tsarki na Ubangiji, zai kawo ga Ubangiji rago daga garke wanda ba shi da lahani saboda yin hadaya don laifinsa. Za a kimata kuɗinsa bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri. Hadaya ce ta laifi.
If a soul commits a trespass, and sins unwittingly in the holy things of Jehovah, then he shall bring his trespass offering to Jehovah, a ram without blemish out of the flock, according to thy estimation in silver by shekels, after the shekel of the sanctuary, for a trespass offering.
16 Dole yă biya abin da ya kāsa yi dangane da abubuwa masu tsarki, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar abin a kan wannan sa’an nan yă ba wa firist. Firist kuwa zai yi kafara dominsa da ragon hadaya don laifi. Za a kuwa gafarta masa.
And he shall make restitution for that which he has done amiss in the holy thing, and shall add the fifth part to it, and give it to the priest. And the priest shall make atonement for him with the ram of the trespass offering, and he shall be forgiven.
17 “In mutum ya yi zunubi, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, ko da yake bai sani ba, shi mai laifi ne. Za a kuwa nemi hakki daga gare shi.
And if a soul sins, and does any of the things which Jehovah has commanded not to be done, though he did not know it, yet he is guilty, and shall bear his iniquity.
18 Zai kawo wa firist rago daga garke, marar lahani. Za a kimanta tamanin rago daidai da tamanin hadaya don laifi. Firist kuwa zai yi kafara don kuskuren da mutumin ya yi ba da saninsa ba, za a gafarta masa.
And he shall bring a ram without blemish out of the flock, according to thy estimation, for a trespass offering, to the priest. And the priest shall make atonement for him concerning the thing by which he erred unwittingly and knew it not, and he shall be forgiven.
19 Hadaya ce ta laifi, ya yi laifi na abin da ya yi marar kyau ga Ubangiji.”
It is a trespass offering. He is certainly guilty before Jehovah.