< Firistoci 5 >

1 “‘Mutum zai yi zunubi in bai yi magana ba sa’ad da ya ji ana shelar neman shaida game da wani abin da ya gani ko kuwa ya ji, alhakin zai zauna a wuyansa.
“Zgriješi li tko tako što čuje riječi proklinjanja a odbije da svjedoči iako je mogao biti svjedokom jer je ili sam vidio ili doznao pa tako nosi krivnju na sebi;
2 “‘Ko kuwa in mutum ya taɓa wani abin da yake mai ƙazanta, ko gawar naman jeji marar tsabta, ko na shanu marar tsabta, ko na halittu marasa tsabtan da suke motsi a ƙasa; ko da yake bai sani ba, ya ƙazantu ke nan, kuma ya yi laifi.
ili ako tko dirne kakav nečist predmet, strv nečiste zvijeri, strv nečista živinčeta ili strv nečista puzavca - i u neznanju postane nečist i odgovoran;
3 Ko kuwa in ya taɓa rashin tsabta na mutane, wani abin da zai sa shi rashin tsabta; ko da yake bai sani ba, sa’ad da ya gane, zai zama mai laifi.
ili kad se tko dotakne nečistoće čovječje, bilo to što mu drago od čega se nečistim postaje i toga ne bude svjestan, kad dozna, biva odgovoran;
4 Ko kuwa in mutum bai yi tunani ba, ya yi rantsuwar yin wani abu, ko mai kyau ko marar kyau; ko da yake bai sani ba, duk da haka sa’ad da ya gane zai zama mai laifi.
nadalje, kad tko nepromišljeno izusti zakletvu na dobro ili zlo - na što se već čovjek nepromišljeno zaklinje - i toga ne bude svjestan, onda, kad dozna, biva odgovoran;
5 Sa’ad da wani yana da laifi a kowanne cikin waɗannan hanyoyi, dole yă furta a hanyar da ya yi zunubin
ako, dakle, tko postane odgovoran u bilo čemu od toga, neka prizna počinjeni grijeh.
6 kuma don zunubin da ya yi, dole yă kawo wa Ubangiji tunkiya ko akuya daga garke kamar hadaya don zunubi; firist kuwa zai yi kafara dominsa da kuma domin zunubinsa.
I neka prinese Jahvi kao žrtvu naknadnicu za počinjeni grijeh jednu ženku od sitne stoke, janje ili kozle, kao žrtvu okajnicu. Neka svećenik izvrši nad njim obred pomirenja koji će ga osloboditi od njegova grijeha.”
7 “‘In ba zai iya kawo tunkiyar ba, sai yă kawo kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu ga Ubangiji a matsayin hakki don zunubinsa, ɗaya domin hadaya don zunubi ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa.
“Ako mu sredstva ne dopuštaju da pribavi glavu sitne stoke, neka Jahvi, kao naknadnicu za počinjeni grijeh, prinese dvije grlice ili dva golubića; jedno kao žrtvu okajnicu, a drugo kao žrtvu paljenicu.
8 Zai kawo su wa firist, wanda da fari zai miƙa ɗaya domin hadaya don zunubi. Zai murɗe kan daga wuyanta, ba tare da tsinke kan gaba ɗaya ba,
Neka ih donese svećeniku, a on neka najprije prinese ono što je određeno kao žrtva okajnica. Stisnuvši ga za vrat, neka mu slomi šiju, ali neka glave ne otkida.
9 zai kuma yayyafa jinin hadaya don zunubin a gefen bagade; a tsiyaye sauran jinin kuma a gindin bagade. Hadaya ce ta zunubi.
Neka krvlju žrtve poškropi žrtvenik sa strane, a ostatak krvi neka se iscijedi podno žrtvenika. To je žrtva okajnica.
10 Firist zai miƙa ɗayan matsayin hadaya ta ƙonawa bisa ga yadda aka tsara, yă kuma yi kafara dominsa saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta masa.
Onda neka drugo prinese kao žrtvu paljenicu prema propisu. Neka tako svećenik nad tim čovjekom izvrši obred pomirenja za grijeh koji je počinio, i bit će mu oprošteno.
11 “‘In ba zai iya kawo kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu ba, sai yă kawo humushin garwan gari mai laushi domin hadaya don zunubi. Ba lalle ba ne yă sa mai ko turare a kansa, saboda wannan hadaya ce ta zunubi.
Ako mu sredstva ne dopuštaju da pribavi dvije grlice ili dva golubića, neka Jahvi, u zadovoljštinu za počinjeni grijeh, prinese jednu desetinu efe njaboljeg brašna. Ulja u nj neka ne ulijeva niti na nj tamjana stavlja jer je žrtva okajnica.
12 Zai kawo wa firist, firist kuwa zai ɗiba da hannu don yă kasance abin tunawa, sai yă ƙone a bisan bagaden kamar hadayar da ake ƙona da wuta ga Ubangiji. Hadaya ce ta zunubi.
Kada to donese svećeniku, neka svećenik zagrabi punu pregršt kao spomen-žrtvu i na žrtveniku sažeže u čast Jahvi povrh paljenih žrtava. To je žrtva okajnica.
13 Ta haka firist zai yi kafara dominsa saboda dukan waɗannan zunuban da ya yi, za a kuwa gafarta masa. Sauran hadayar za tă zama ta firist, kamar yadda yake bisa ga hadaya ta gari.’”
Neka tako svećenik izvrši nad tim čovjekom obred pomirenja za grijeh koji je počinio u bilo kojem od tih slučajeva, pa će mu biti oprošteno. Ono ostalo neka pripadne svećeniku kao i od žrtve prinosnice.”
14 Ubangiji ya ce wa Musa,
Još reče Jahve Mojsiju:
15 “Sa’ad da mutum ya ci amana, ya kuma yi zunubi ba da gangan ba dangane da wani cikin abubuwa masu tsarki na Ubangiji, zai kawo ga Ubangiji rago daga garke wanda ba shi da lahani saboda yin hadaya don laifinsa. Za a kimata kuɗinsa bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri. Hadaya ce ta laifi.
“Ako tko počini pronevjerenje ogriješivši se nehotično o svete stvari Jahvine, neka za naknadu, kao žrtvu naknadnicu, prinese Jahvi, iz svoga stada, ovna bez mane, vrijedna - po tvojoj procjeni - najmanje dva šekela srebra - prema cijeni hramskog šekela.
16 Dole yă biya abin da ya kāsa yi dangane da abubuwa masu tsarki, yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar abin a kan wannan sa’an nan yă ba wa firist. Firist kuwa zai yi kafara dominsa da ragon hadaya don laifi. Za a kuwa gafarta masa.
Neka nadoknadi koliko se ogriješio o svete stvari i tome doda još petinu i neka dadne svećeniku. Neka svećenik nad njim izvrši obred pomirenja ovnom žrtve naknadnice, i bit će mu oprošteno.
17 “In mutum ya yi zunubi, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, ko da yake bai sani ba, shi mai laifi ne. Za a kuwa nemi hakki daga gare shi.
Ako tko i ne znajući pogriješi i učini štogod što je Jahve zabranio, kriv je, pa neka snosi posljedice svoje krivnje.
18 Zai kawo wa firist rago daga garke, marar lahani. Za a kimanta tamanin rago daidai da tamanin hadaya don laifi. Firist kuwa zai yi kafara don kuskuren da mutumin ya yi ba da saninsa ba, za a gafarta masa.
Neka svećeniku dovede za naknadnicu iz svoga stada ovna bez mane, prema tvojoj procjeni. Neka svećenik nad tim čovjekom izvrši obred pomirenja za pogrešku što je počinio u neznanju, i bit će mu oprošteno.
19 Hadaya ce ta laifi, ya yi laifi na abin da ya yi marar kyau ga Ubangiji.”
To je žrtva naknadnica; on je doista bio odgovoran Jahvi.”

< Firistoci 5 >