< Firistoci 4 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Još reèe Gospod Mojsiju govoreæi:
2 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da wani ya yi zunubi ba da gangan ba, har ya karya ɗaya daga cikin dokokin Ubangiji,
Kaži sinovima Izrailjevim, i reci: ako ko zgriješi nehotice i uèini štogod što je Gospod zabranio da se ne èini,
3 “‘In shafaffen firist ya yi zunubi, ya jawo wa jama’a laifi, dole yă kawo wa Ubangiji ɗan bijimi marar lahani a matsayin hadaya don zunubi saboda zunubin da ya yi.
Ako sveštenik pomazani zgriješi, te bude na grijeh narodu, neka za grijeh svoj koji je uèinio prinese tele zdravo Gospodu na žrtvu za grijeh.
4 Zai kawo bijimin a ƙofar Tentin Sujada a gaban Ubangiji. Zai ɗibiya hannunsa a kan bijimin, yă kuma yanka shi a gaban Ubangiji.
I dovedavši tele na vrata šatoru od svjedoèanstva pred Gospoda, neka metne ruku svoju teletu na glavu, i zakolje tele pred Gospodom.
5 Sa’an nan shafaffen firist zai ɗiba jinin bijimin yă kai cikin Tentin Sujada.
I neka uzme sveštenik pomazani krvi od teleta, i unese je u šator od sastanka.
6 Yă tsoma yatsarsa a cikin jinin, yă kuma yafa sau bakwai a gaban Ubangiji, a gaban labulen wuri mai tsarki.
I neka zamoèi sveštenik prst svoj u krv, i krvlju sedam puta pokropi pred Gospodom pred zavjesom od svetinje.
7 Sa’an nan firist ɗin zai zuba jinin a ƙahonin bagaden turare masu ƙanshi da suke a gaban Ubangiji a Tentin Sujada. Sauran jinin bijimin zai zuba a gindin bagaden hadaya ta ƙonawa a ƙofar zuwa Tentin Sujada.
I neka pomaže sveštenik tom krvlju rogove oltaru, na kom se kadi mirisima pred Gospodom u šatoru od sastanka, a ostalu krv od teleta svu neka izlije na podnožje oltaru, na kom se pale žrtve na vratima šatora od sastanka.
8 Zai cire dukan kitsen daga bijimin hadaya don zunubi, kitsen da ya rufe kayan cikin, ko kuwa da suka shafe su,
I neka izvadi sve salo iz teleta za grijeh, salo što pokriva crijeva i sve salo što je na crijevima;
9 da ƙodoji biyu tare da kitsen da yake kansu kusa da kwiɓi, da kuma murfin hanta, waɗanda zai cire tare da ƙodoji.
I oba bubrega, i salo što je na njima i na slabinama, i mrežicu na jetri s bubrezima neka izvadi,
10 Zai cire su daidai kamar yadda akan cire na bijimin hadaya ta salama. Sai firist ɗin yă ƙone su a kan bagaden ƙona hadaya.
Onako kako se vadi iz goveèeta za žrtvu zahvalnu; i neka zapali sveštenik na oltaru, na kom se žrtva pali.
11 Amma fatar ɗan bijimin, da namansa, da kansa, da ƙafafunsa, da kayan cikinsa, da hanjinsa,
A kožu od teleta i sve meso s glavom i s nogama i crijeva i balegu,
12 wato, dukan sauran bijimi, dole yă ɗauke su zuwa waje da sansani zuwa wani wuri mai tsabta inda ake zub da toka, yă ƙone shi a itacen da yake cin wuta a tarin toka.
I cijelo tele neka iznese napolje iz okola na èisto mjesto, gdje se prosipa pepeo, i neka ga spali ognjem na drvima; na mjestu gdje se prosipa pepeo neka se spali.
13 “‘In dukan jama’ar Isra’ilawa suka yi zunubi ba da gangan ba, har suka aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, ko da yake jama’ar ba su san batun ba, duk da haka sun yi laifi.
Ako li bi sav zbor sinova Izrailjevih zgriješio nehotice i ne bi zbor znao za to, i uèinili bi štogod što je Gospod zabranio da se ne èini, te bi skrivili,
14 Sa’ad da suka gane da zunubin da suka aikata, dole taron su kawo ɗan bijimi a matsayin hadaya don zunubi, su kawo shi a gaban Tentin Sujada.
Kad se dozna za grijeh koji su uèinili, onda neka zbor prinese tele na žrtvu za grijeh, i neka ga dovedu pred šator od sastanka.
15 Dattawan jama’a za su ɗibiya hannuwansu a kan bijimin a gaban Ubangiji, sai a yanka bijimin a gaban Ubangiji.
I starješine od zbora neka metnu teletu na glavu ruke svoje pred Gospodom, i sveštenik neka zakolje tele pred Gospodom.
16 Sa’an nan shafaffen firist zai ɗibi jinin bijimi zuwa cikin Tentin Sujada.
I sveštenik pomazani neka unese krvi od teleta u šator od sastanka,
17 Zai tsoma yatsarsa cikin jini yă kuma yayyafa shi a gaban Ubangiji sau bakwai a gaban labule.
I neka sveštenik zamoèi prst svoj u krv, i sedam puta pokropi pred Gospodom pred zavjesom.
18 Zai zuba jinin a ƙahonin bagaden da suke gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada. Zai zuba sauran jinin a gindin bagaden hadaya ta ƙonawa a ƙofar zuwa Tentin Sujada.
I tom krvlju neka pomaže rogove oltaru koji je pred Gospodom u šatoru od sastanka, a ostalu krv svu neka izlije na podnožje oltaru na kom se pali žrtva, na vratima šatora od sastanka.
19 Zai cire dukan kitsen daga gare shi yă ƙone a kan bagade,
A sve salo izvadivši iz njega neka zapali na oltaru.
20 yă kuma yi da wannan bijimi kamar yadda ya yi da bijimi na hadaya don zunubi. Ta haka firist zai yi kafara dominsu, za a kuwa gafarta musu.
I s tijem teletom neka èini onako kako èini s teletom za svoj grijeh, tako neka uèini s njim; tako æe ih sveštenik oèistiti od grijeha, i oprostiæe im se.
21 Sa’an nan zai ɗauki bijimin waje da sansani yă ƙone shi kamar yadda ya ƙone bijimi na fari. Wannan ita ce hadaya don zunubi domin jama’a.
A tele neka iznese napolje iz okola, i spali ga kao i prvo tele; to je žrtva za grijeh svega zbora.
22 “‘Sa’ad da shugaba ya yi zunubi ba da gangan ba, har ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji Allahnsa ya umarta, to, ya yi laifi.
Ako li poglavar zgriješi, i uèini nehotice štogod što je Gospod Bog njegov zabranio da se ne èini, te skrivi,
23 Sa’ad da aka sanar da shi game da zunubin da ya yi, dole yă kawo bunsuru marar lahani a matsayin hadayarsa.
Kad dozna za grijeh svoj, koji je uèinio, tada neka dovede na žrtvu jare muško, zdravo.
24 Zai ɗibiya hannunsa a kan bunsurun yă kuma yanka shi a inda ake yankan hadayar ƙonawa a gaban Ubangiji. Hadaya ce ta zunubi.
I neka metne ruku svoju jaretu na glavu, i sveštenik neka ga zakolje gdje se kolje žrtva paljenica pred Gospodom; to je žrtva za grijeh.
25 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin hadaya don zunubi da yatsarsa yă sa a ƙahonin bagaden hadayar ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a gindin bagade.
I neka uzme sveštenik krvi od žrtve za grijeh na prst svoj, i pomaže rogove oltaru na kom se žrtva pali; a ostalu krv neka izlije na podnožje oltaru na kom se žrtva pali.
26 Zai ƙone dukan kitse a kan bagade kamar yadda ya ƙone kitsen hadaya ta salama. Ta haka firist zai yi kafara saboda zunubin mutumin, za a kuwa gafarta masa.
A sve salo neka zapali na oltaru kao salo od žrtve zahvalne; i tako æe ga oèistiti sveštenik od grijeha njegova, i oprostiæe mu se.
27 “‘In wani memba a cikin jama’a ya yi zunubi ba da gangan ba, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, to, ya yi laifi.
Ako li ko iz prostoga naroda zgriješi nehotice, i uèini štogod što je Gospod zabranio da se ne èini, te skrivi,
28 Sa’ad da aka sanar da shi game da zunubin da ya yi, dole yă kawo akuya marar lahani a matsayin hadayarsa domin zunubin da ya yi.
Kad dozna za grijeh svoj, koji je uèinio, tada neka dovede na žrtvu jare žensko zdravo za grijeh, koji je uèinio.
29 Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya don zunubin yă kuma yanka ta a inda ake hadaya ta ƙonawa.
I neka metne ruku svoju na glavu žrtvi za grijeh, i neka je sveštenik zakolje na mjestu gdje se kolje žrtva paljenica.
30 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin da yatsarsa yă zuba a ƙahoni a bagaden hadaya ta ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a ƙasan bagade.
I neka uzme sveštenik krvi od nje na prst svoj, i pomaže rogove oltaru na kom se pali žrtva; a ostalu krv svu neka izlije na podnožje oltaru.
31 Za a ɗebe kitsenta duka kamar yadda akan ɗebe kitsen hadaya ta salama. Firist zai ƙona shi a kan bagaden don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Ta haka firist zai yi kafara dominsa, za a kuwa gafarta masa.
I sve salo iz nje neka izvadi kao što se vadi salo iz žrtve zahvalne, i neka ga zapali sveštenik na oltaru za ugodni miris Gospodu; a tako æe ga oèistiti od grijeha sveštenik, i oprostiæe mu se.
32 “‘Idan kuwa daga cikin’yan tumaki zai ba da hadayarsa, sai ya kawo’yar tunkiya marar lahani.
Ako li bi doveo izmeðu ovaca na žrtvu za grijeh, neka dovede žensko zdravo.
33 Zai ɗibiya hannunsa a kanta yă kuma yanka ta hadaya don zunubi a inda ake yankan hadayar ƙonawa.
I neka metne ruku svoju na glavu žrtvi za grijeh, i neka je sveštenik zakolje na mjestu gdje se kolje žrtva paljenica.
34 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin hadaya don zunubin da yatsarsa yă zuba a ƙahonin bagaden hadayar ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a gindin bagade.
I neka uzme sveštenik krvi od žrtve za grijeh na prst svoj, i neka pomaže rogove oltaru na kom se pali žrtva; a ostalu krv svu neka izlije na podnožje oltaru.
35 Zai kuma ɗebe kitsenta duka kamar yadda a kan ɗebe na ragon hadaya ta salama. Firist zai ƙone shi a bisa bagaden a bisa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ta haka firist ɗin zai yi kafara dominsa saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta masa.
I sve salo neka izvadi kao što se vadi salo iz jagnjeta za žrtvu zahvalnu; i neka ga sveštenik zapali na oltaru za žrtvu ognjenu Gospodu; i tako æe ga oèistiti sveštenik od grijeha njegova, koji je uèinio, i oprostiæe mu se.