< Firistoci 4 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And he spoke Yahweh to Moses saying.
2 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da wani ya yi zunubi ba da gangan ba, har ya karya ɗaya daga cikin dokokin Ubangiji,
Speak to [the] people of Israel saying anyone that it will sin by inadvertence any of all [the] commandments of Yahweh which not they will be done and he will do any one of them.
3 “‘In shafaffen firist ya yi zunubi, ya jawo wa jama’a laifi, dole yă kawo wa Ubangiji ɗan bijimi marar lahani a matsayin hadaya don zunubi saboda zunubin da ya yi.
If the priest anointed he will sin to [the] guilt of the people and he will present on sin his which he sinned a bull a young one of [the] herd unblemished to Yahweh to a sin offering.
4 Zai kawo bijimin a ƙofar Tentin Sujada a gaban Ubangiji. Zai ɗibiya hannunsa a kan bijimin, yă kuma yanka shi a gaban Ubangiji.
And he will bring the bull to [the] entrance of [the] tent of meeting before Yahweh and he will lean hand his on [the] head of the bull and he will cut [the] throat of the bull before Yahweh.
5 Sa’an nan shafaffen firist zai ɗiba jinin bijimin yă kai cikin Tentin Sujada.
And he will take the priest anointed some of [the] blood of the bull and he will bring it into [the] tent of meeting.
6 Yă tsoma yatsarsa a cikin jinin, yă kuma yafa sau bakwai a gaban Ubangiji, a gaban labulen wuri mai tsarki.
And he will dip the priest finger his in the blood and he will spatter some of the blood seven times before Yahweh with [the] face of [the] curtain of the holy place.
7 Sa’an nan firist ɗin zai zuba jinin a ƙahonin bagaden turare masu ƙanshi da suke a gaban Ubangiji a Tentin Sujada. Sauran jinin bijimin zai zuba a gindin bagaden hadaya ta ƙonawa a ƙofar zuwa Tentin Sujada.
And he will put the priest some of the blood on [the] horns of [the] altar of [the] incense of the perfume before Yahweh which [is] in [the] tent of meeting and - all [the] blood of the bull he will pour out to [the] base of [the] altar of burnt offering which [is] [the] entrance of [the] tent of meeting.
8 Zai cire dukan kitsen daga bijimin hadaya don zunubi, kitsen da ya rufe kayan cikin, ko kuwa da suka shafe su,
And all [the] fat of [the] bull of the sin offering he will lift up from it the fat which covers over the entrails and all the fat which [is] on the entrails.
9 da ƙodoji biyu tare da kitsen da yake kansu kusa da kwiɓi, da kuma murfin hanta, waɗanda zai cire tare da ƙodoji.
And [the] two the kidneys and the fat which [is] on them which [is] on the loins and the lobe on the liver on the kidneys he will remove it.
10 Zai cire su daidai kamar yadda akan cire na bijimin hadaya ta salama. Sai firist ɗin yă ƙone su a kan bagaden ƙona hadaya.
Just as it is lifted up from [the] ox of [the] sacrifice of the peace offering and he will make smoke them the priest on [the] altar of burnt offering.
11 Amma fatar ɗan bijimin, da namansa, da kansa, da ƙafafunsa, da kayan cikinsa, da hanjinsa,
And [the] hide of the bull and all flesh its with head its and with legs its and entrails its and offal its.
12 wato, dukan sauran bijimi, dole yă ɗauke su zuwa waje da sansani zuwa wani wuri mai tsabta inda ake zub da toka, yă ƙone shi a itacen da yake cin wuta a tarin toka.
And he will bring out all the bull to from [the] outside of the camp to a place pure to [the] pouring out of the fatty ash and he will burn it on wood with fire at [the] pouring out of the fatty ash it will be burned.
13 “‘In dukan jama’ar Isra’ilawa suka yi zunubi ba da gangan ba, har suka aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, ko da yake jama’ar ba su san batun ba, duk da haka sun yi laifi.
And if all [the] congregation of Israel they will go astray and it will be hidden [the] matter from [the] eyes of the assembly and they will do one of all [the] commandments of Yahweh which not they will be done and they will be guilty.
14 Sa’ad da suka gane da zunubin da suka aikata, dole taron su kawo ɗan bijimi a matsayin hadaya don zunubi, su kawo shi a gaban Tentin Sujada.
And it will be made known the sin which they have sinned on it and they will present the assembly a bull a young one of [the] herd to a sin offering and they will bring it before [the] tent of meeting.
15 Dattawan jama’a za su ɗibiya hannuwansu a kan bijimin a gaban Ubangiji, sai a yanka bijimin a gaban Ubangiji.
And they will lean [the] elders of the congregation hands their on [the] head of the bull before Yahweh and someone will cut [the] throat of the bull before Yahweh.
16 Sa’an nan shafaffen firist zai ɗibi jinin bijimi zuwa cikin Tentin Sujada.
And he will bring the priest anointed some of [the] blood of the bull into [the] tent of meeting.
17 Zai tsoma yatsarsa cikin jini yă kuma yayyafa shi a gaban Ubangiji sau bakwai a gaban labule.
And he will dip the priest finger his some of the blood and he will spatter [it] seven times before Yahweh with [the] face of the curtain.
18 Zai zuba jinin a ƙahonin bagaden da suke gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada. Zai zuba sauran jinin a gindin bagaden hadaya ta ƙonawa a ƙofar zuwa Tentin Sujada.
And some of the blood he will put - on [the] horns of the altar which [is] before Yahweh which [is] in [the] tent of meeting and all the blood he will pour out to [the] base of [the] altar of burnt offering which [is] [the] entrance of [the] tent of meeting.
19 Zai cire dukan kitsen daga gare shi yă ƙone a kan bagade,
And all fat its he will lift up from it and he will make [it] smoke the altar towards.
20 yă kuma yi da wannan bijimi kamar yadda ya yi da bijimi na hadaya don zunubi. Ta haka firist zai yi kafara dominsu, za a kuwa gafarta musu.
And he will do to the bull just as he did to [the] bull of the sin offering so he will do to it and he will make atonement on them the priest and it will be forgiven to them.
21 Sa’an nan zai ɗauki bijimin waje da sansani yă ƙone shi kamar yadda ya ƙone bijimi na fari. Wannan ita ce hadaya don zunubi domin jama’a.
And he will bring out the bull to from [the] outside of the camp and he will burn it just as he burned the bull first [is] [the] sin offering of the assembly it.
22 “‘Sa’ad da shugaba ya yi zunubi ba da gangan ba, har ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji Allahnsa ya umarta, to, ya yi laifi.
That a leader he will sin and he will do one of all [the] commandments of Yahweh God his which not they will be done by inadvertence and he will be guilty.
23 Sa’ad da aka sanar da shi game da zunubin da ya yi, dole yă kawo bunsuru marar lahani a matsayin hadayarsa.
Or it has been made known to him sin his which he has sinned by it and he will bring present his a male goat of goats a male unblemished.
24 Zai ɗibiya hannunsa a kan bunsurun yă kuma yanka shi a inda ake yankan hadayar ƙonawa a gaban Ubangiji. Hadaya ce ta zunubi.
And he will lean hand his on [the] head of the male goat and he will cut [the] throat of it in [the] place where someone cuts [the] throat of the burnt offering before Yahweh [is] a sin offering it.
25 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin hadaya don zunubi da yatsarsa yă sa a ƙahonin bagaden hadayar ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a gindin bagade.
And he will take the priest some of [the] blood of the sin offering on finger his and he will put [it] on [the] horns of [the] altar of burnt offering and blood its he will pour out to [the] base of [the] altar of burnt offering.
26 Zai ƙone dukan kitse a kan bagade kamar yadda ya ƙone kitsen hadaya ta salama. Ta haka firist zai yi kafara saboda zunubin mutumin, za a kuwa gafarta masa.
And all fat its he will make smoke the altar towards like [the] fat of [the] sacrifice of the peace offering and he will make atonement on him the priest from sin his and it will be forgiven to him.
27 “‘In wani memba a cikin jama’a ya yi zunubi ba da gangan ba, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, to, ya yi laifi.
And if a person one it will sin by inadvertence one of [the] people of the land when does it one of [the] commandments of Yahweh which not they will be done and he will be guilty.
28 Sa’ad da aka sanar da shi game da zunubin da ya yi, dole yă kawo akuya marar lahani a matsayin hadayarsa domin zunubin da ya yi.
Or it has been made known to him sin his which he has sinned and he will bring present his a female goat of goats unblemished a female on sin his which he has sinned.
29 Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya don zunubin yă kuma yanka ta a inda ake hadaya ta ƙonawa.
And he will lean hand his on [the] head of the sin offering and he will cut [the] throat of the sin offering in [the] place of the burnt offering.
30 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin da yatsarsa yă zuba a ƙahoni a bagaden hadaya ta ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a ƙasan bagade.
And he will take the priest some of blood its on finger his and he will put [it] on [the] horns of [the] altar of burnt offering and all blood its he will pour out to [the] base of the altar.
31 Za a ɗebe kitsenta duka kamar yadda akan ɗebe kitsen hadaya ta salama. Firist zai ƙona shi a kan bagaden don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Ta haka firist zai yi kafara dominsa, za a kuwa gafarta masa.
And all fat its he will remove just as it was removed [the] fat from on [the] sacrifice of the peace offering and he will make [it] smoke the priest the altar towards to an odor of soothing to Yahweh and he will make atonement on him the priest and it will be forgiven to him.
32 “‘Idan kuwa daga cikin’yan tumaki zai ba da hadayarsa, sai ya kawo’yar tunkiya marar lahani.
And if a male lamb he will bring present his to a sin offering a female unblemished he will bring it.
33 Zai ɗibiya hannunsa a kanta yă kuma yanka ta hadaya don zunubi a inda ake yankan hadayar ƙonawa.
And he will lean hand his on [the] head of the sin offering and he will cut [the] throat of it to a sin offering in [the] place where someone cuts [the] throat of the burnt offering.
34 Sa’an nan firist zai ɗibi jinin hadaya don zunubin da yatsarsa yă zuba a ƙahonin bagaden hadayar ƙonawa, yă kuma zuba sauran jinin a gindin bagade.
And he will take the priest some of [the] blood of the sin offering on finger his and he will put [it] on [the] horns of [the] altar of burnt offering and all blood its he will pour out to [the] base of the altar.
35 Zai kuma ɗebe kitsenta duka kamar yadda a kan ɗebe na ragon hadaya ta salama. Firist zai ƙone shi a bisa bagaden a bisa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ta haka firist ɗin zai yi kafara dominsa saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta masa.
And all fat its he will remove just as it is removed [the] fat of the young ram from [the] sacrifice of the peace offering and he will make smoke the priest them the altar towards on [the] fire offerings of Yahweh and he will make atonement on him the priest on sin his which he has sinned and it will be forgiven to him.

< Firistoci 4 >