< Firistoci 3 >
1 “‘In hadayar wani mutum, hadaya ta salama ce, ya kuma miƙa’yar dabba daga garke, ko namiji ko ta mace ce, sai yă miƙa dabbar da ba ta da lahani a gaban Ubangiji.
And if his oblation be a sacrifice of peace offerings; if he offer of the herd, whether male or female, he shall offer it without blemish before the LORD.
2 Yă kuma ɗibiya hannunsa bisa kan hadayarsa, yă yanka ta a mashigin Tentin Sujada. Sa’an nan’ya’yan Haruna waɗanda suke firistoci za su yayyafa jinin a kan bagade a kowane gefe.
And he shall lay his hand upon the head of his oblation, and kill it at the door of the tent of meeting: and Aaron’s sons the priests shall sprinkle the blood upon the altar round about.
3 Daga hadaya ta zumuncin da zai kawo, sai a miƙa waɗannan hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a wuta; wato, dukan kitsen da ya rufe kayan ciki ko kuwa da sun shafe su,
And he shall offer of the sacrifice of peace offerings an offering made by fire unto the LORD; the fat that covereth the inwards, and all the fat that is upon the inwards,
4 da ƙodoji biyu tare da kitsen da yake kansu kusa da kwiɓi, da kuma murfin hanta waɗanda zai cire tare da ƙodoji.
and the two kidneys, and the fat that is on them, which is by the loins, and the caul upon the liver, with the kidneys, shall he take away.
5 ’Ya’yan Haruna za su ƙone shi a kan bagade a bisa hadaya ta ƙonawa wadda take a kan itacen da yake cin wuta, kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
And Aaron’s sons shall burn it on the altar upon the burnt offering, which is upon the wood that is on the fire: it is an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.
6 “‘In ya miƙa dabba ce daga garke a matsayin hadaya ta salama ga Ubangiji, zai miƙa namiji ko ta mace marar lahani.
And if his oblation for a sacrifice of peace offerings unto the LORD be of the flock; male or female, he shall offer it without blemish.
7 In ya miƙa ɗan rago ne, zai kawo shi a gaban Ubangiji.
If he offer a lamb for his oblation, then shall he offer it before the LORD:
8 Zai ɗibiya hannu a kan hadayarsa, yă yanka shi a gaban Tentin Sujada. Sa’an nan’ya’yan Haruna maza za su yayyafa jinin dabbar a kowane gefe na bagade.
and he shall lay his hand upon the head of his oblation, and kill it before the tent of meeting: and Aaron’s sons shall sprinkle the blood thereof upon the altar round about.
9 Daga hadaya ta zumuncin zai kawo, sai a miƙa waɗannan hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a wuta, wato, kitsen, ƙibabbiya wutsiyar gaba ɗaya da ya yanka gab da ƙashin gadon baya, dukan kitsen da ya rufe kayan ciki, ko kuwa da suka shafe su,
And he shall offer of the sacrifice of peace offerings an offering made by fire unto the LORD; the fat thereof, the fat tail entire, he shall take it away hard by the backbone; and the fat that covereth the inwards, and all the fat that is upon the inwards,
10 da ƙodoji biyu tare da kitsen da yake kansu kusa da kwiɓi, da kuma murfin hanta waɗanda zai cire tare da ƙodoji.
and the two kidneys, and the fat that is upon them, which is by the loins, and the caul upon the liver, with the kidneys, shall he take away.
11 Firist zai ƙone su a kan bagade kamar hadayar abinci, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
And the priest shall burn it upon the altar: it is the food of the offering made by fire unto the LORD.
12 “‘In yana miƙa akuya ce, zai kawo ta a gaban Ubangiji.
And if his oblation be a goat, then he shall offer it before the LORD:
13 Zai ɗibiya hannunsa a kanta yă kuma yanka ta a gaban Tentin Sujada. Sa’an nan’ya’yan Haruna maza za su yayyafa jininta a kowane gefe na bagade.
and he shall lay his hand upon the head of it, and kill it before the tent of meeting: and the sons of Aaron shall sprinkle the blood thereof upon the altar round about.
14 Daga abin da zai miƙa sai a miƙa waɗannan hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a wuta, wato, dukan kitsen da ya rufe kayan cikin, ko kuwa da suka shafe su,
And he shall offer thereof his oblation, [even] an offering made by fire unto the LORD; the fat that covereth the inwards, and all the fat that is upon the inwards,
15 da ƙodoji biyu tare da kitsen da yake kansu kusa da kwiɓi, da kuma murfin hanta waɗanda zai cire tare da ƙodoji.
and the two kidneys, and the fat that is upon them, which is by the loins, and the caul upon the liver, with the kidneys, shall he take away.
16 Firist zai ƙone su a kan bagade kamar abinci, hadaya ce da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi. Dukan kitsen na Ubangiji ne.
And the priest shall burn them upon the altar: it is the food of the offering made by fire, for a sweet savour: all the fat is the LORD’S.
17 “‘Wannan dawwammamiyar farilla ce ga tsararraki masu zuwa, a inda za ku zauna. Ba za ku ci wani kitse ko wani jini ba.’”
It shall be a perpetual statute throughout your generations in all your dwellings, that ye shall eat neither fat nor blood.