< Firistoci 27 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
2 “Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Duk sa’ad da mutum ya yi rantsuwa ta musamman zai keɓe wani ga Ubangiji, ta wurin biyan kuɗaɗen fansa,
“İsrail halkına de ki, ‘Eğer bir kimse RAB'be birini adamışsa senin biçeceğin değeri ödeyerek adağını yerine getirebilir.
3 ga yadda ma’aunin biyan zai kasance, mutum mai shekara tsakanin ashirin da sittin, za a biya azurfa hamsin.
Bu değerler şöyle olacak: Yirmi yaşından altmış yaşına kadar erkekler için elli kutsal yerin şekeli gümüş,
4 Mace kuma za a biya azurfa talatin.
kadınlar için otuz şekel.
5 Saurayi mai shekara tsakanin biyar da ashirin, za a biya azurfa ashirin, yarinya kuma azurfa goma.
Beş yaşından yirmi yaşına kadar erkekler için yirmi, kadınlar için on şekel.
6 Yaro mai shekara tsakanin wata ɗaya da shekara biyar, za a biya azurfa biyar,’yar yarinya kuma azurfa uku.
Bir aylıktan beş yaşına kadar oğlanlar için beş, kızlar için üç şekel gümüş.
7 Namijin da ya fi shekara sittin, za a biya azurfa goma sha biyar, mace kuma azurfa goma.
Eğer altmış ya da daha yukarı yaşta iseler, erkekler için on beş, kadınlar için on şekel.
8 In mai alkawarin matalauci ne da ba zai iya biyan ƙayyadadden abin da aka tsara ba, sai yă tafi wurin firist, shi firist kuma yă duba yadda mutumin da ya yi alkawarin zai iya biya. Sa’an nan mutumin zai biya abin da firist ya faɗa.
Ancak adakta bulunan kişi belirtilen parayı ödeyemeyecek kadar yoksulsa, adadığı kişiyi kâhine götürecek; kâhin adakta bulunan kişinin ödeme gücüne göre ona değer biçecektir.
9 “‘In abin da ya yi alkawarin yardajje ne a matsayin hadaya ga Ubangiji, wannan dabbar da aka bayar ga Ubangiji, za tă zama mai tsarki.
“‘RAB'be sunulacak adak O'na sunu olarak sunulabilecek hayvanlardan biriyse, kabul edilecektir. O'na böyle sunulan her hayvan kutsaldır.
10 Kada yă yi musayarta ko yă yi musaya mai kyau da marar kyau, ko marar kyau da mai kyau; in lalle ne yă yi musayar dabbar da wata, to, duk wannan da kuma wanda zai yi musayar da ita za su zama masu tsarki.
Adakta bulunan kişi RAB'be sunacağı adağı değiştirmemeli. İyisinin yerine kötüsünü ya da kötüsünün yerine iyisini koymamalı. Eğer hayvanı değiştirirse, değiştirilen hayvanların ikisi de kutsal sayılacaktır.
11 In abin da ya yi alkawari dabba ce marar tsarki, wadda ba yardajje ba ce, a matsayin hadaya ga Ubangiji, dole a kai dabbar wa firist,
Eğer adak RAB'be sunulamayacak kirli sayılan hayvanlardan biriyse, kâhine götürülecektir.
12 wanda zai yanke hukunci dacewarta, ko mai kyau ce, ko marar kyau. Duk darajar da firist ya kimanta, haka za tă zama.
Hayvan iyi ya da kötü olsun, kâhin ona değer biçecek. Biçilen değer neyse o geçerli olacak.
13 In mai shi yana so yă fanshi dabbar, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajarta.
Ama sahibi hayvanı geri almak isterse, kâhinin biçtiği değerin üzerine beşte bir fazlasını katarak ödemelidir.
14 “‘In mutum ya miƙa gidansa a matsayin wani abu mai tsarki ga Ubangiji, firist zai daidaita dacewar ko mai kyau ne, ko marar kyau. Duk darajar da firist ya kimanta, haka za tă zama.
“‘Bir kimse kutsal bir sunu olarak evini RAB'be adarsa, evin iyi ya da kötü olduğuna kâhin karar verecektir. Kâhinin biçtiği değer geçerli olacaktır.
15 In mutumin da ya keɓe gidansa ya fanshe shi, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar, gidan kuma zai zama nasa.
Eğer kişi adadığı evi geri almak isterse, kâhinin biçtiği değerin üzerine beşte bir fazlasını katarak ödeyecek, böylece ev kendisine kalacaktır.
16 “‘In wani ya keɓe wa Ubangiji wani sashe daga cikin gonarsa ta gādo, sai yă kimanta kuɗin gonar daidai da yawan irin da za a iya shuka a gonar. Za a kimanta kuɗin a kan shekel hamsin na irin sha’ir.
“‘Bir kimse ailesinden kalan tarlanın bir bölümünü RAB'be adamak isterse, tarlaya ekilecek tohum miktarına göre değer biçilecektir. Bir homer arpa tohumu ekilebilecek tarlanın değeri elli şekel gümüş olacaktır.
17 In ya keɓe gonarsa a Shekara ta Murna, darajar da aka kimanta za tă zauna.
Eğer tarlasını özgürlük yılından hemen sonra adarsa, bu fiyat geçerli olacaktır.
18 Amma in ya keɓe gonar bayan Shekara ta Murnan, firist zai kimanta darajar bisa ga yawan shekarun da suka rage har zuwa Shekara ta Murna mai zuwa, sai a rage darajar da aka kimanta a kanta.
Eğer özgürlük yılından daha sonra adarsa, kâhin bir sonraki özgürlük yılına kadar geçecek yılların sayısına göre tarlaya değer biçecektir. Tarlanın fiyatı daha düşük olacaktır.
19 In mutumin da ya keɓe gonar, yana so yă fanshe ta, to, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajarta, gonar kuwa tă zama nasa.
Kişi tarlasını geri almak isterse, tarlaya biçilen değerin üzerine beşte bir fazlasını katarak ödeyecek, böylece tarla kendisine kalacaktır.
20 In kuma bai fanshe gonar ba, ko kuwa in ya sayar wa wani dabam, ba za a taɓa fanshe ta ba.
Ama tarlayı geri almadan başka birine satarsa, tarla geri alınamaz.
21 Sa’ad da aka saki gonar a Shekara ta Murna, za tă zama mai tsarki, a matsayin gonar da aka miƙa ga Ubangiji, za tă zama mallakar firistoci.
Tarla özgürlük yılında serbest kaldığı zaman, RAB'be koşulsuz adanmış bir tarla gibi kutsal sayılacak ve kâhinlere ait olacaktır.
22 “‘In mutum ya keɓe gonar da ya saya, wadda take ba sashe na gonar iyali ba, ga Ubangiji,
“‘Bir kimse ailesinin mülkü olmayan, sonradan satın aldığı bir tarlayı RAB'be adarsa,
23 firist zai kimanta darajarta har Shekara ta Murna, dole kuma mutumin yă biya darajarta a ranar, a matsayin wani abu mai tsarki ga Ubangiji.
kâhin özgürlük yılına kadar geçecek yıllara göre ona bir değer biçecektir. O gün kişi biçilen değer üzerinden ödeme yapacak ve para RAB'be ait olacak, kutsal sayılacaktır.
24 A Shekara ta Murna ɗin, gonar za tă dawo ga mutumin da aka saye ta daga wurinsa, wanda yake mai gonar.
Özgürlük yılında tarla ilk sahibine geri verilecektir.
25 A kimanta kowace daraja bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri, gera ashirin ga shekel.
Değer biçilirken kutsal yerin şekeli esas alınacaktır. Bir şekel yirmi geradır.
26 “‘Ba wani da zai iya keɓe ɗan farin dabba, da yake ɗan fari ya riga ya zama na Ubangiji, ko na saniya, ko na tunkiya, na Ubangiji ne.
“‘İlk doğan hayvan RAB'be aittir. İster sığır, ister davar olsun, kimse onu RAB'be adayamaz. Çünkü o RAB'bindir.
27 In tana cikin dabbobin da suke marasa tsarki, zai iya saye ta a darajar da aka kimanta, yă ƙara da kashi ɗaya bisa biyar na darajarta. In bai fanshe ta ba, sai a sayar da ita a darajar da aka kimanta.
Ama ilk doğan hayvan kirli sayılan hayvanlardan biriyse, kişi kâhinin biçeceği değerin beşte bir fazlasını ödeyerek hayvanı geri alabilir. Geri alınmazsa, hayvan biçilen değer üzerinden başka birine satılacaktır.
28 “‘Amma babu abin da mutum ya mallaka, ya kuma keɓe ga Ubangiji, ko mutum ne, ko dabba, ko ganar iyali da za a sayar, ko a fansa; kome da aka keɓe a wannan hanya, mafi tsarki ne ga Ubangiji.
“‘İster insan, ister hayvan, ister aileden kalma tarla olsun, RAB'be koşulsuz adanan hiç bir şey satılmayacak ve geri alınmayacaktır. Çünkü RAB'be koşulsuz adanan her şey RAB için çok kutsaldır.
29 “‘Babu wani da aka keɓe don hallaka da za a fansa; dole a kashe shi.
RAB'be koşulsuz adanan insan para karşılığında kurtarılamayacak, kesinlikle öldürülecektir.
30 “‘Ushirin kome daga gona, ko hatsi daga ƙasa, ko’ya’yan itatuwa daga itatuwa, na Ubangiji ne, mai tsarki ne ga Ubangiji.
“‘İster toprağın ürünü, ister ağacın meyvesi olsun, toprakta yetişen her şeyin ondalığı RAB'be aittir. RAB için kutsaldır.
31 In mutum ya fanshi wani zakansa, dole yă ƙara kashi ɗaya bisa biyar na darajar.
Kim ondalığının bir bölümünü geri almak isterse, değerinin üzerine beşte bir fazlasını katarak ödemelidir.
32 Ushirin gaba ɗaya na garken shanu, da na tumaki, kowane kashi ɗaya bisa goma na dabbar da ta wuce ƙarƙashin sandan mai kiwo, za tă zama mai tsarki ga Ubangiji.
Bütün sığırlarla davarların ondalığı, sayımda çoban değneğinin altından geçen her onuncu hayvan RAB için kutsal sayılacaktır.
33 Kada kuwa ya zaɓa mai kyau daga marar kyau, ko yă yi musaya. In ya yi musaya kuwa, dabbar da wadda ya musayar, za su zama masu tsarki, ba kuma za a fanshe su ba.’”
Hayvan sahibi hayvanları iyi, kötü diye ayırmayacak, birini öbürüyle değiştirmeyecektir. Değiştirirse, değiştirilen hayvanların ikisi de kutsal sayılacak ve karşılığı ödenip geri alınamayacaktır.’”
34 Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa a Dutsen Sinai saboda Isra’ilawa.
RAB'bin Sina Dağı'nda İsrail halkı için Musa'ya bildirdiği buyruklar bunlardır.

< Firistoci 27 >