< Firistoci 26 >
1 “‘Kada ku yi gumaka, ko ku kafa siffa, ko al’amudi wa kanku, kada kuma ku sa sassaƙaƙƙun duwatsu a ƙasarku don ku rusuna musu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Kik ulos kido moro amora mopa kata chungo siro moro milamo bende kidi moro amora mopa kik yud e pinyu kukulorune kulame. An e Jehova Nyasaye ma Nyasachu.
2 “‘Ku kiyaye Asabbataina, ku kuma ba wa wuri mai tsarkina girma. Ni ne Ubangiji.
Rituru Sabato maga, kendo luoruru kara maler mar lemo. An e Jehova Nyasaye.
3 “‘In kuka kiyaye farillaina, kuka yi biyayya da umarnaina,
Ka urito buchena kendo urito chikena,
4 zan aika da ruwan sama a lokacinsa, ƙasa kuma za tă ba da hatsi, itatuwa kuma za su haihu’ya’yansu.
to abiro kelonu koth e kinde mowinjore, kendo pinyu nochieg cham mi yiendeu nonyag olembe.
5 Masussukanku za su ci gaba har lokacin girbin inabi, girbin inabi kuma zai ci gaba har lokacin shuki, za ku kuma ci duk abincin da kuke so cikin salama a ƙasarku.
Ubiro dino cham nyaka chop kinde muponoe mzabibu kendo ubiro pono mzabibu nyaka chop kinde muchwoyoe bende ubiro bedo gi chiemo moromou kendo ubiro dak gi kwe e pinyu.
6 “‘Zan ba ku salama a ƙasar, za ku kuwa kwanta, kuma babu wani da zai tsorata ku. Zan kori mugayen namun jeji daga ƙasar, takobi kuma ba zai ratsa cikin ƙasarku ba.
Anamiu kwe e pinyu, mi ununindi maonge ngʼama nomiu luoro. Anatieki ondiegi duto e dieru kendo ligangla ok nomonju kata matin.
7 Za ku kori abokan gābanku, za su kuwa fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
Unuriemb jowasiku duto e dieru kendo ununeg-gi.
8 Mutanenku biyar za su kori mutum ɗari, mutanenku ɗari kuma za su kori mutane dubu goma, abokan gābanku kuma za su fāɗi a kaifin takobi a gabanku.
Jou abich nobed gi teko mar riembo ji mia achiel, kendo jou mia achiel nobed gi teko mar riembo ji gana apar, kendo ununeg wasiku.
9 “‘Zan dube ku da idon rahama, in kuma sa ku riɓaɓɓanya ku kuma ƙaru, zan kiyaye alkawarina da ku.
Abiro olonu gweth, kendo abiro miyo unywol mi ununyaa mathoth, kendo abiro chopo singruok duto mane atimo kodu.
10 Za ku ci gaba da cin girbin bara, har ku fitar da shi don ku sami wurin saboda sabo.
Cham mag higa makadho manie decheu noromu chamo nyaka chop kinde ma ugologie oko mondo uyud thuolo mar rwako cham manyien.
11 Zan kafa wurin zamana a cikinku, ba zan kuma yi ƙyamarku ba.
Abiro loso kar dakna e dieru kendo ok anajwangʼu kata matin.
12 Zan yi tafiya a cikinki in kuma zama Allahnku, za ku kuwa zama mutanena.
Anawuoth e dieru mi nabed Nyasachu, kendo unubed joga.
13 Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar don kada ku ƙara zama bayi ga Masarawa; na karya sandunan wahalarku, na kuma bar ku ku yi tafiya a sake.
An e Jehova Nyasaye ma Nyasachu mane ogolou e piny Misri, mondo kik ubed wasumb jo-Misri kendo ne aturo lodi mane otwenu mi koro sani uwuotho tir.
14 “‘Amma in za ku kasa kunne gare ni, ku kuma aikata dukan waɗannan umarnai,
To ka unutamru winja ma ok urito chikenago duto,
15 in kuka kuma ƙi farillaina, kuka yi ƙyamar dokokina, kuka kuma kāsa kiyaye umarnaina, har kuka karya alkawarina,
ma udagi buchena kendo uchayo chikena, ma ok urito chikena duto ma uketho singruok mara mane atimo kodu,
16 to, zan yi muku wannan. Zan kawo muku abin bantsoro, cututtuka da zazzaɓin da zai lalatar da idonku, yă kuma sa ranku a wahala. Za ku shuka iri a banza, domin abokan gābanku ne za su ci.
to koro ngʼeuru chuth ni mae e kaka abiro timonu: Anapou gi masira kod tho marach, gi tuo mayuyo wangʼ gi tuo mamiyo del dhe. Cham ma upidho ok nokonyu kata matin nikech jowasiku ema nochamgi.
17 Zan yi gāba da ku har abokan gābanku su ci ku a yaƙi, su waɗanda suke ƙinku za su yi mulki a kanku, za ku gudu ba tare da wani yana korinku ba.
Anabed ka asin kodu mi wasiku nolou e lweny kendo gininegu; unubed e bwo loch jowasiku, kendo unubwogru gi ngʼwech kata kaonge joma lawou.
18 “‘In bayan dukan wannan, ba ku saurare ni ba, zan hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
Kata bangʼ timo magi duto kapod ok unyal winja, to anakumu nyadibiriyo kuom richo duto.
19 Zan karya ikonku wanda kuke fariya da shi, in hana ruwan sama, ƙasa kuma tă zama kamar tagulla.
Anatiek sunga mar wich teko ma un-go, kendo anami polo rieny ka chuma, kendo piny mwalo nodog matek ka mula.
20 Ƙarfinku zai ƙare a banza domin ƙasarku ba za tă ba da hatsi ba, balle itatuwan ƙasar su ba da’ya’ya.
Ubiro ketho tekreu kayiem nono, kuchwoyo cham nimar chambu ok nochiegi, kata yedheu bende ok nonyag olembe.
21 “‘In kuka ci gaba da tayar mini, kuka ƙi ku saurare ni, zan ninka wahalolinku sau bakwai, yadda ya dace da zunubanku.
Kapod usikona mana gi wich teko kendo udagi winja, to anakelnu masiche moloyo nyadibiriyo maromre gi richou.
22 Zan aika da mugayen namun jeji a kanku, za su kuwa kashe’ya’yanku, su hallaka shanunku, su rage yawanku, ku zama kaɗan. Wannan zai sa a rasa mutane a kan hanyoyinku.
Abiro oronu le mag bungu mondo oked kodu kendo ginineg nyithindo kaachiel gi jambu mi unudongʼ manok kendo yoreu nodongʼ nono maonge joma wuothoe.
23 “‘In duk da waɗannan abubuwa, ba ku yarda da gyaran da nake yi muku ba, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
Kobedo ni pod ok udwogo ira kata bangʼ timonu magi duto, kendo udhi mana nyime gi wich teko,
24 zan yi adawa da ku, zan kuma aukar muku saboda zunubanku har sau bakwai.
to an bende nanyisu wich teko, mi anamiu kum moloyo nyadibiriyo nikech richou.
25 Zan kawo takobi a kanku don in yi ramuwa saboda karya alkawarin da kuka yi. Sa’ad da kuka janye zuwa cikin biranenku, zan aika da annoba a cikinku, za a kuwa ba da ku ga hannun abokan gāba.
Kendo anakel lweny e dieru mondo achulgo kuor kuom ketho singruok mane atimo kodu, kendo kinde duto manuchokru e miechu to nagou gi tuoche kendo wasiku nomaku.
26 Sa’ad da na yanke abincinku, mata goma za su dafa abinci a murhu ɗaya, za su kuma rarraba abincin a ma’auni. Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba.
Anami chiembu doko manok kendo mon apar notedi e agulu achiel. Ginipimnu chiemo e rapim, kendo kata kuchiemo to onge ngʼama noyiengʼ.
27 “‘In duk da haka kuka ci gaba da ƙin saurare ni, kuka ci gaba da yin adawa da ni,
Kobedo ni pod ok udwogo ira kata bangʼ timonu magi duto, kendo udhi mana nyime gi wich teko,
28 cikin fushina, sai in yi adawa da ku, in kuma hukunta ku saboda zunubanku har sau bakwai.
to an bende nasik kodu gi wich teko gi mirimba mager, kendo anakumu moloyo nyadibiriyo gi mirimba mager nikech richou.
29 Za ku ci naman’ya’yanku maza da na’ya’yanku mata.
Unucham ring yawuotu kod nyiwu.
30 Zan rurrushe dukan masujadanku, in yanke bagadanku na turare, in yi tarin gawawwakinku a kan gumakanku, zan kuma yi ƙyamarku.
Anaketh kuondeu motingʼore gi malo, kendo anamuki kendeu muwangʼoe ubani. Anaket ringreu motho kuom nyiseche manono kendo anajwangʼu chuth.
31 Zan mai da biranenku kango, in lalace wuraren tsarkinku, ba zan kuma shaƙi ƙanshi hadayunku ba.
Miechu madongo biro bedo gundni, kuondeu maler mag lemo abiro ketho, kendo ok anayie winjo tik mangʼwe ngʼar mag misengini mau.
32 Zan mai da ƙasarku kango har abokan gābanku da suke zama a wurin su yi mamaki.
Anaketh pinyu kendo jowasiku mabiro dakie nohum nono.
33 Zan watsar da ku cikin al’ummai, in kuma ja takobina in kore ku. Ƙasarku za tă zama kufai, biranenku kuma su zama kango.
Abiro keyou e kind ogendini, anagol ligangla mi alawu. Pinyu nodongʼ gunda, kendo miechu madongo nokethi chuth.
34 Sa’an nan ƙasar za tă ji daɗin hutun shekarun Asabbacinta, a dukan lokutan da take kango, ku kuwa kuna a ƙasar abokan gābanku, sa’an nan ƙasar za tă huta ta ji daɗin asabbatanta.
E kinde duto ma pinyu nodongʼ gunda, ka un to asekeyou udak e kind wasiku; pinyu nobed ma ok opur mondo ochulgo Sabato maga duto mane ok urito.
35 A dukan lokutan da take kango, ƙasar za tă sami hutun da ba tă samu a lokutan asabbatan da kuke zama a cikinta ba.
E kinde duto ma pinyu nodongʼ gunda kamano, enobed ma ok opure, ka oritogo Sabato duto mane ok oyweyoe e kinde mane udak kuno.
36 “‘Ga waɗanda za su ragu kuwa, zan cika zukatansu da tsoro a ƙasashen abokan gābansu har motsin ganyen da iska ta hura zai sa su ruga da gudu. Za su yi gudu kamar suna gudu daga takobi ne, za su kuma fāɗi, ko da yake babu wanda yake korinsu.
To kuom jou modongʼ ka ngima e piny wasikgi, ginto anagogi kod kihondko e piny wasikgi, ma kata ka yamo okwadho it oboke maponi giwinjo, to giniwuog gi ngʼwech. Giniringi mana ka joma wasigu lawo gi ligangla mi gipodh piny kata obedo ni onge ngʼama lawogi.
37 Za su yi karo da juna kamar waɗanda suke tsere wa takobi, ko da yake babu wanda yake korinsu. Ta haka ba za ku iya tsaya a gaban abokan gābanku ba.
Ginituomre kendgi giwegi mana ka joma wasigu lawo gi ligangla, kata obedo ni onge ngʼama lawogi. Omiyo ok unuyud teko mar kedo gi wasiku.
38 Za ku mutu a cikin al’ummai, ƙasar abokan gābanku za tă cinye ku.
Unulal nono e kind ogendini, kendo wasiku notieku.
39 Sauranku da suka ragu za su lalace a ƙasashen abokan gābansu saboda zunubansu; da kuma saboda zunuban kakanninsu.
Joma otony e dieru mane odongʼ kangima e pinje mag wasiku nobed ka dendgi dhi adhiya nikech richogi kendo nikech richo mag kweregi, mana machal kaka notimore ni kweregi.
40 “‘Amma in suka tuba daga zunubansu da zunuban kakanninsu, da cin amanar da suka yi mini, da kuma adawar da suka yi da ni,
Bangʼ mae gibiro hulo richogi gi richo kweregi mane omiyo giweya kaachiel gi richo mane omiyo gibedo wasika,
41 waɗanda suka sa na yi adawa da su har da na aika da su ƙasar abokan gābansu, sa’ad da suka ƙasƙantar da zukatansu marasa kaciya, suka kuma biya hukuncin zunubansu,
mane omiyo abedo kodgi mamon kendo mane omiyo aterogi e piny wasikgi, eka bangʼe chunygi ma ok oyie kaka adwaro nobolre, mi giniyud kum kuom richogi,
42 zan tuna da alkawarina da Yaƙub, da alkawarina da Ishaku, da kuma alkawarina da Ibrahim, zan tuna da ƙasar.
eka abiro paro singruok mane atimo gi Jakobo kendo gi Isaka kendo gi Ibrahim, kendo anapar pinyu.
43 Gama za su gudu su bar ƙasar, ƙasar kuwa ta ji daɗin asabbatanta yayinda take kango muddin ba su ciki. Za su biya hukuncin zunubansu domin sun ƙi dokokina, suka kuma yi ƙyamar farillaina.
Piny to nodongʼ gunda nikech joma odakie osea, kendo obiro nindo ka ok opure mondo ochulgo Sabato duto mane ok oyweyoe. Giniyud kum kuom richogi nikech ne gichayo chikena kod buchena.
44 Duk da haka, sa’ad da suke a ƙasar abokan gābansu, ba zan ƙi su, ko in yi ƙyamarsu, in hallaka su ƙaƙaf, har in karya alkawarina da su ba. Ni ne Ubangiji Allahnsu.
“Kata kamano, kata obedo ni gin e piny wasikgi, to ka anawitgi kendo ok anajwangʼ-gi kata tiekogi chuth, mi aketh singruok mane atimo kodgi. An Jehova Nyasaye ma Nyasachgi.
45 Amma saboda su, zan tuna da alkawarin da na yi da kakanninsu, waɗanda na fitar da su daga Masar a idon al’ummai, don in zama Allahnsu. Ni ne Ubangiji.’”
Nikech aherogi, omiyo anapar singruok mane atimo gi kweregi, mane agolo e piny Misri mana kane ogendini neno mondo an Jehova Nyasaye abed Nyasachgi.”
46 Waɗannan su ne farillai, da dokoki, da kuma ƙa’idodin da Ubangiji ya kafa a Dutsen Sinai, tsakaninsa da Isra’ilawa ta wurin Musa.
Magi e buche, chike kod yore mane Jehova Nyasaye omiyo jo-Israel e Got Sinai kokadho kuom Musa.