< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
“İsrail halkına buyruk ver, kandilin sürekli yanıp ışık vermesi için saf sıkma zeytinyağı getirsinler.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Harun kandilleri benim huzurumda, Buluşma Çadırı'nda, Levha Sandığı'nın önündeki perdenin dışında, akşamdan sabaha kadar sürekli yanar biçimde tutacak. Kuşaklar boyunca sürekli bir kural olacak bu.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
RAB'bin huzurunda saf altın kandillikteki kandiller sürekli yanacaktır.”
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
“İnce undan on iki pide pişireceksin. Her biri efanın onda ikisi ağırlığında olacak.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
Bunları RAB'bin huzurunda iki sıra halinde, altışar altışar saf altın masanın üzerine dizeceksin.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
İki sıra ekmeğin yanına anma payı olarak saf günnük koyacaksın. Bu RAB için yakılan sunu olacak ve ekmeğin yerini alacak.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Bu ekmek, İsrail halkı adına sonsuza dek sürecek bir antlaşma olarak, her Şabat Günü aksatılmadan RAB'bin huzurunda dizilecek.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
Ve Harun'la oğullarına ait olacak. Onu kutsal bir yerde yiyecekler. Çünkü çok kutsaldır. RAB için yakılan sunulardan onların sürekli bir payı olacak.”
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
İsrailliler arasında annesi İsrailli babası Mısırlı bir adam vardı. Ordugahta onunla bir İsrailli arasında kavga çıktı.
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
İsrailli kadının oğlu RAB'be sövdü, lanet etti. Onu Musa'ya getirdiler. Annesi Dan oymağından Divri'nin kızı Şelomit'ti.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
Adamı göz altına alıp RAB'bin kararını beklediler.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
“Onu ordugahın dışına çıkar. Ettiği laneti duyan herkes elini adamın başına koysun ve bütün topluluk onu taşlasın.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
İsrail halkına de ki, ‘Kim Tanrısı'na lanet ederse günahının cezasını çekecektir.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
RAB'be söven kesinlikle öldürülecektir. Bütün topluluk onu taşlayacak. İster yerli ister yabancı olsun, RAB'be söven herkes öldürülecektir.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
“‘Adam öldüren kesinlikle öldürülecektir.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Başkasının hayvanını öldüren, yerine bir hayvan vererek aldığı canın karşılığını canla ödeyecektir.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Kim komşusunu yaralarsa, kendisine de aynı şey yapılacaktır.
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
Kırığa karşılık kırık, göze göz, dişe diş olmak üzere, ona ne yaptıysa kendisine de aynı şey yapılacaktır.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Hayvan öldüren yerine bir hayvan verecek, adam öldüren öldürülecektir.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Yerli yabancı herkes için tek bir yasanız olacak. Tanrınız RAB benim.’”
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Musa bunları İsrail halkına bildirdikten sonra, halk RAB'be lanet eden adamı ordugahın dışına çıkardı ve taşlayarak öldürdü. Böylece İsrail halkı RAB'bin Musa'ya verdiği buyruğu yerine getirmiş oldu.

< Firistoci 24 >