< Firistoci 24 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Och Herren talade med Mose, och sade:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Bjud Israels barnom, att de bära till dig klara stötta bomoljo till lysning, hvilken dagliga skall slås upp i lamporna,
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Utanför vittnesbördsens förlåt i vittnesbördsens tabernakel. Och Aaron skall sköta det både afton och morgon för Herranom dagliga. Det skall vara en evig rätt med edra efterkommande.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Och skall han pynta till lamporna på den sköna ljusastakanom för Herranom dagliga.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
Och du skall taga semlomjöl, och baka deraf tolf kakor; en kaka skall hålla två tiungar;
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
Och skall lägga dem, ju sex i hvar hop, på det sköna bordet för Herranom;
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
Och skall lägga på dem rent rökelse, att det skall vara åminnelsebröd till ett offer Herranom.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
På hvar Sabbathsdag skall han pynta dem till Herranom alltid, af Israels barn till ett evigt förbund;
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
Och skola höra Aaron och hans söner till, de skola äta dem på heligt rum; ty det är hans aldrahelgasta af Herrans offer till en evig rätt.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
Och en man utgick, enes Israelitiska qvinnos son, den ens Egyptisk mans son var ibland Israels barn, och trätte med en Israelitisk man i lägret;
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
Och nämnde Namnet, och bannades. Då hade de honom fram för Mose. Och hans moder het Selomith, Dibri dotter, af Dans slägte.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
Och de lade honom i fängelse, tilldess dem vorde viss svar gifven genom Herrans mun.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Och Herren talade med Mose, och sade:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
För honom ut för lägret, som bannats hafver, och låt alla dem som det hörde, lägga sina händer på hans hufvud, och låt hela menigheten stena honom.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Och säg Israels barnom: Hvilken som bannar sin Gud, han skall bära sina synd.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
Hvilken som Herrans Namn nämner, han skall döden dö; hela menigheten skall stena honom. Såsom utländningen, så skall ock inländningen vara; om han nämner det Namnet, så skall han dö.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Om någor slår ena mennisko, han skall döden dö;
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Men den som slår någon boskap, han skall betalat kropp för kropp;
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Och den som gör sinom nästa skada, honom skall man göra såsom han gjorde:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
Skada för skada, öga för öga, tand för tand; såsom han hafver gjort ene mennisko skada, så skall man göra honom igen;
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Så att den som slår någon boskap, den skall betalat; men den som slår ena mennisko, han skall dö.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Samma rätten skall vara ibland eder, så för utländningen, som för inländningen; ty jag är Herren edar Gud.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Och Mose sade detta för Israels barnom, och förde honom, som bannats hade, ut för lägret, och stenade honom. Och alltså gjorde Israels barn, såsom Herren Mose budit hade.