< Firistoci 24 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
И рече Господь к Моисею, глаголя:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
заповеждь сыном Израилевым, да возмут ти елей от масличия чист исцежен в светение, да горит светило всегда,
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
вне завесы в скинии свидения, и возжигати будут его Аарон и сынове его от вечера до заутра пред Господем непрестанно, законно вечно в роды вашя:
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
на светилнице чистем возжигати будете светила пред Господем даже до утра.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
И возмете муки пшеничны, и сотворите от нея дванадесять хлебов: дву десятин да будет хлеб един:
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
и возложите их на два положения, по шести хлебов едино положение на трапезе чисте пред Господем:
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
и возложите на едино положение ливан чист и соль, и да будут хлебы в память предлежащыя пред Господем:
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
в день субботы да предлагаются пред Господем всегда от сынов Израилевых, завет вечный:
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
и да будут Аарону и сыном его, и да снедят я на месте святе, суть бо святая святых: сие им от жертв Господу в закон вечный.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
И изыде сын жены Израилтяныни, и сей бе сын Египтянина в сынех Израилевых: и пряхуся в полце иже от Израилтяныни и муж Израилтянин:
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
и нарек сын жены Израилтяныни имя (Господне) прокля. И приведоша его к Моисею. Имя же матере его Саломииф, дщерь Давриина, от племене Данова.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
И ввергоша его в темницу, разсудити о нем повелением Господним.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
И рече Господь к Моисею, глаголя:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
изведи клявшаго вне полка, и да возложат вси слышавшии руце свои на главу его, и да побиют его камением весь сонм:
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
и сыном Израилевым глаголи и речеши к ним: человек человек, иже аще прокленет Бога своего, грех приимет:
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
нарицаяй же имя Господне смертию да умрет: камением да побиют его весь сонм израильский: аще туземец, или пришлец, егда наречет имя Господне, да умрет:
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
и человек, иже аще поразит всяку душу человечу, и умрет, смертию да умрет:
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
и иже аще ударит скота, и умрет, да воздаст душу вместо души:
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
и аще кто сотворит порок ближнему, якоже сотвори ему, такожде и ему да сотворят:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
изломление за изломление, око за око, зуб за зуб: якоже сотворил порок человеку, такожде да сотворят и ему:
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
иже аше ударит человека, и умрет смертию да умрет:
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
оправдание едино будет пришелцу и туземцу, яко Аз есмь Господь Бог ваш.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
И глагола Моисей к сыном Израилевым, и изведоша клявшаго вне полка, и побиша его камением весь сонм: и сынове Израилевы сотвориша, якоже заповеда Господь Моисею.