< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Byd Israels barn at de skal la dig få ren olje av støtte oliven til lysestaken, så lampene kan settes op til enhver tid.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Utenfor vidnesbyrdets forheng i sammenkomstens telt skal Aron alltid holde dem i stand fra aften til morgen for Herrens åsyn; det skal være en evig lov for eder, fra slekt til slekt.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
På lysestaken av rent gull skal han alltid holde lampene i stand for Herrens åsyn.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
Du skal ta fint mel og bake tolv kaker av det; hver kake skal være to tiendedeler av en efa.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
Og du skal legge dem i to rader, seks i hver rad, på bordet av rent gull for Herrens åsyn.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
Og du skal legge ren virak på hver rad, og den skal være et ihukommelses-offer for brødene, et ildoffer for Herren.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
På hver sabbatsdag skal brødene gjennem alle tider legges frem for Herrens åsyn; det skal være en gave fra Israels barn - en evig pakt.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
De skal høre Aron og hans sønner til, og de skal ete dem på et hellig sted; for de er høihellige og er hans del av Herrens ildoffer - en evig rettighet.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
En mann som var sønn av en israelittisk kvinne, men hadde en egypter til far, gikk engang ut blandt Israels barn. Da kom den israelittiske kvinnes sønn og en israelittisk mann i trette med hverandre i leiren,
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
og den israelittiske kvinnes sønn spottet Herrens navn og bannet det, og de førte ham til Moses. Hans mor hette Selomit, Dibris datter, av Dans stamme.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
De satte ham fast, forat de kunde få avgjørelse ved et ord fra Herren.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Før spotteren utenfor leiren, og alle de som hørte det, skal legge sine hender på hans hode, og hele menigheten skal stene ham.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Og du skal tale til Israels barn og si: Når nogen banner sin Gud, skal han lide for sin synd.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
Og den som spotter Herrens navn, skal late livet, hele menigheten skal stene ham; enten det er en fremmed eller en innfødt, skal han stenes når han spotter Herrens navn.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Når en slår et menneske ihjel, skal han late livet.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Men den som slår et stykke fe ihjel, skal godtgjøre det, liv for liv.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Når nogen volder sin næste mén på hans legeme, skal der gjøres det samme med ham som han selv har gjort:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
brudd for brudd, øie for øie, tann for tann; det samme mén som han volder en annen, skal han selv få.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Den som slår et stykke fe ihjel, skal godtgjøre det; men den som slår et menneske ihjel, skal late livet.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
En og samme rett skal gjelde for eder, den skal gjelde for den fremmede som for den innfødte; for jeg er Herren eders Gud.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Og Moses sa dette til Israels barn, og de førte spotteren utenfor leiren og stenet ham - Israels barn gjorde som Herren hadde befalt Moses.

< Firistoci 24 >