< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Commande aux fils d’Israël qu’ils t’apportent de l’huile d’olive pure, broyée, pour le luminaire, afin de faire brûler la lampe continuellement.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Aaron l’arrangera devant l’Éternel, continuellement, du soir au matin, en dehors du voile du témoignage, dans la tente d’assignation: [c’est] un statut perpétuel en vos générations;
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
il arrangera les lampes sur le chandelier pur, devant l’Éternel, continuellement.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
Et tu prendras de la fleur de farine, et tu en cuiras douze gâteaux: chaque gâteau sera de deux dixièmes;
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
et tu les placeras en deux rangées, six par rangée, sur la table pure, devant l’Éternel,
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
et tu mettras de l’encens pur sur [chaque] rangée; et ce sera un pain de mémorial, un sacrifice par feu à l’Éternel.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Chaque jour de sabbat on les arrangera devant l’Éternel, continuellement, de la part des fils d’Israël: [c’est] une alliance perpétuelle.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
Et cela appartiendra à Aaron et à ses fils, et ils le mangeront dans un lieu saint; car ce lui sera une chose très sainte d’entre les sacrifices de l’Éternel faits par feu: [c’est] un statut perpétuel.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
Et le fils d’une femme israélite (mais il était fils d’un homme égyptien), sortit parmi les fils d’Israël; et le fils de la femme israélite et un homme israélite se battirent dans le camp;
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
et le fils de la femme israélite blasphéma le Nom et [le] maudit; et on l’amena à Moïse. Or le nom de sa mère était Shelomith, fille de Dibri, de la tribu de Dan.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
Et on le mit sous garde, afin de décider [de son sort], selon la parole de l’Éternel.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Et l’Éternel parla à Moïse, disant:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Fais sortir hors du camp celui qui a maudit; et que tous ceux qui l’ont entendu posent leurs mains sur sa tête, et que toute l’assemblée le lapide.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Et tu parleras aux fils d’Israël, en disant: Tout homme qui aura maudit son Dieu, portera son péché;
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
et celui qui blasphémera le nom de l’Éternel sera certainement mis à mort: toute l’assemblée ne manquera pas de le lapider; on mettra à mort tant l’étranger que l’Israélite de naissance, lorsqu’il aura blasphémé le Nom.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Et si quelqu’un a frappé à mort un homme, il sera certainement mis à mort.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Et celui qui aura frappé à mort une bête, fera compensation, vie pour vie.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Et si un homme a causé quelque mal corporel à son prochain, il lui sera fait comme il a fait:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
fracture pour fracture, œil pour œil, dent pour dent; selon le mal corporel qu’il aura causé à un homme, ainsi il lui sera fait.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Celui qui frappera [à mort] une bête, fera compensation pour elle, et celui qui aura frappé [à mort] un homme, sera mis à mort.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Il y aura une même loi pour vous: il en sera de l’étranger comme de l’Israélite de naissance; car moi, je suis l’Éternel, votre Dieu.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Et Moïse parla aux fils d’Israël, et ils firent sortir hors du camp celui qui avait maudit, et le lapidèrent avec des pierres. Et les fils d’Israël firent comme l’Éternel avait commandé à Moïse.

< Firistoci 24 >