< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said to Moses/me,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
“Command the Israeli people to continually bring to you clear oil made from pressed olives to burn in the lamps [in the Sacred Tent], in order that those lamps will burn all the time.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Outside the curtain of the Very Holy Place, Aaron must take care of the lamps in my presence continually, in order that they will burn all during the night. That regulation must be obeyed forever.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Those lampstands that burn in my presence must be taken care of continually.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
“Also, [each week] you must take some fine flour and bake twelve [very big] loaves of bread, using about four quarts/liters of flour for each loaf.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
Put the loaves in two rows, with six loaves in each row, on the table covered with pure gold, in my presence.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
Along each row, place [in some gold cups] some pure incense to be burned to be an offering to me instead of the bread.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
New/Fresh loaves of bread must be put [on the table] each Sabbath day, to signify the agreement that will never end, that I have made with you Israeli people.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
The bread [that is taken off the table] belongs to Aaron and his sons. They must eat it in a holy place, because it is a very holy part of the offerings that are given to me by being burned.”
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
There was a man whose mother’s name was Shelomith; she was an Israeli whose father was Dibri from the tribe of Dan. And that man’s father was from Egypt. One day that man and another Israeli man started to fight inside the camp. And while they were fighting, that man cursed Yahweh [MTY].
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
So the Israeli people seized him and guarded him until they could find out what Yahweh would reveal to them [that they should do to that man].
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Then Yahweh said to Moses/me,
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
“[Tie up and] take outside the camp the man who has cursed me. There all those who heard what he said must put their hands on his head [to indicate that he is guilty], and then all the people must [kill him by] throwing stones at him.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Tell the Israelis, ‘If anyone curses me, he must (endure the consequences/be punished).
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
So anyone who curses me [MTY] must be executed. All the people must throw stones at him. It does not matter if he is a foreigner or an Israeli citizen; anyone who curses me must be executed.’
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
“Also, If anyone murders another person, he must be executed.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
And anyone who kills [another person’s] animal must give that person a live animal to replace the one that he killed.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
And if one person injures another person, the injured person is allowed to injure the person who injured him in the same way:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
If someone breaks one of another person’s bones, that person is allowed to break one of the bones of the person who injured him. If someone gouges out an eye of another person, that person is allowed to gouge out the eye of the person who injured him. If someone knocks out the tooth of another person, that person is allowed to knock out one of his teeth. What is done to the offender must be the same as what he did to the other person.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Whoever kills [another person’s] animal must give that person a live animal to replace the one that he killed, but anyone who murders another person must be executed.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
That law applies to you Israelis and and also to the foreigners who live among you; I, Yahweh your God [am the one who has commanded it].”
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Then Moses/I told the Israelis [what they must do to the man who cursed Yahweh], so they took the man outside the camp and [killed him by] throwing stones at him. They did what Yahweh commanded Moses/me [to tell them to do].

< Firistoci 24 >