< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Yahweh spake unto Moses, saying:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Command the sons of Israel, That they bring unto thee—pure oil olive, beaten, for giving light, —to cause the lamp to burn up continually.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Outside the veil of the testimony, in the tent of meeting, shall Aaron order it, from evening until morning, before Yahweh continually, —a statute age-abiding, to your generations.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Upon the pure lampstand, shall he order the lamps, —before Yahweh, continually.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
And thou shalt take fine meal, and bake it, in twelve cakes, —of two-tenths, shall each cake be.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
And thou shalt set them in two rows, six in a row, —upon the pure table, before Yahweh.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
And thou shalt put upon each row pure frankincense, —so shall it belong unto the bread as a memorial, an altar-flame unto Yahweh.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Sabbath day by sabbath day, shall he order it before Yahweh continually, —from the sons of Israel as an age-abiding covenant:
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
so shall it be for Aaron and for his sons, and they shall eat it in a holy place, —for most holy, shall it be unto him from among the altar-flames of Yahweh, a statute age-abiding.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
And forth went the son of a woman of Israel—he being the son of a man of Egypt—in the midst of the sons of Israel;
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
and the son of the woman of Israel, and a man of Israel, reviled one another in the camp. And the son of the Israelitish woman uttered contemptuously the Name, and reviled. So they brought him in unto Moses, —now, the name of his mother, was Shelomith, daughter of Dibri, of the tribe of Dan;
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
and they put him in ward, —that a clear answer might be given to them at the mouth of Yahweh.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Then spake Yahweh unto Moses, saying:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Bring forth him that reviled unto the outside of the camp, then shall all that heard [him] lean their hands upon his head, —and all the assembly shall stone him.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
And, unto the sons of Israel, shalt thou speak saying, —What man soever curseth his God shall bear his sin.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
And, he that contemptuously uttereth the name of Yahweh, shall be, surely put to death, all the assembly shall, surely stone, him, —as the sojourner so the home-born, when he contemptuously uttereth the Name, he shall be put to death.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And, when, any man, by smiting taketh the life of any human being, he shall be surely put to death,
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
And he that by smiting taketh away the life of a beast, shall make it good, —life for life.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
And, when, any man, inflicteth a blemish upon his neighbour, as he hath done, so, shall it be done to him:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
fracture for fracture, eye for eye, tooth for tooth, as he inflicteth a blemish upon a human being, so, shall one be inflicted upon him.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And he that killeth a beast, shall make it good, -and he that killeth a human being, shall be put to death.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
One rule, shall ye have, as the sojourner, so the home-born, shall be, —For, I—Yahweh, am your God.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
So then Moses spake unto the sons of Israel, and they took forth the reviler, unto the outside of the camp, and stoned him with stones. Thus, the sons of Israel did, as Yahweh commanded Moses.

< Firistoci 24 >