< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Command the children of Israel, that they bring unto thee pure beaten olive-oil, for the lighting, to cause the lamp to burn continually.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Without the vail of the testimony, in the tabernacle of the congregation, shall Aaron put it in order [for] from evening unto morning before the Lord continually; as a statute for ever in your generations.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Upon the pure candlestick shall be put in order the lamps, before the Lord, continually.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
And thou shalt take fine flour, and bake thereof twelve cakes: of two tenth parts shall each one cake be.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
And thou shalt place them in two rows, six in a row, upon the pure table before the Lord.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
And thou shalt put upon each row pure frankincense, that it may be unto the bread for a memorial, as a fire-offering unto the Lord.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
On every and each sabbath day shall he place it in order before the Lord continually, [obtained] from the children of Israel as an everlasting covenant.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
And it shall belong to Aaron and to his sons; and they shall eat it in a holy place; for it is most holy unto him, from the fire-offerings of the Lord, as a perpetual fixed portion.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
And there went forth a son of an Israelitish woman, but who was the son of an Egyptian man, among the children of Israel; and there quarrelled together in the camp this son of the Israelitish woman and an Israelitish man.
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
And the son of the Israelitish woman pronounced the [holy] Name, and blasphemed; and they brought him unto Moses: [and his mother's name was Shelomith, the daughter of Dibri, of the tribe of Dan; ]
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
And they placed him in ward, until the decision of the Lord could be explained to them.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Lead forth the blasphemer to without the camp; and all that have heard him shall lay their hands upon his head; and all the congregation shall stone him.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
And unto the children of Israel shalt thou speak, saying, Whatsoever man that blasphemeth his God shall bear his sin.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
But he that pronounced the name of the Lord [with blasphemy] shall be put to death, all the congregation shall stone him; be he a stranger, or be he one that is born in the land, when he pronounceth the [holy] Name [with blasphemy, ] he shall be put to death.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And he that taketh the life of any man shall surely be put to death.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
And he that taketh the life of a beast shall make it good: beast for beast.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
And if a man cause a bodily defect in his neighbor, as he hath done, so shall be done to him;
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
Breach for breach, eye for eye, tooth for tooth: in the manner as he hath caused a bodily defect in a man, so shall it be done to him.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And he that killeth a beast, shall make restitution for it; and he that killeth a man, shall be put to death.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
One manner of judicial law shall ye have, the stranger shall be equal with one of your own country; for I am the Lord your God.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And Moses spoke to the children of Israel; and they led forth the blasphemer to without the camp, and they stoned him with stones; and the children of Israel did as the Lord had commanded Moses.

< Firistoci 24 >