< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spake unto Moses, saying,
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Command the children of Israel, that they bring unto thee pure olive oil beaten for the light, to cause a lamp to burn continually.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Without the veil of the testimony, in the tent of meeting, shall Aaron keep it in order from evening to morning before Jehovah continually: it shall be a statute for ever throughout your generations.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
He shall keep in order the lamps upon the pure candlestick before Jehovah continually.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
And thou shalt take fine flour, and bake twelve cakes thereof: two tenth parts [of an ephah] shall be in one cake.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
And thou shalt set them in two rows, six on a row, upon the pure table before Jehovah.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
And thou shalt put pure frankincense upon each row, that it may be to the bread for a memorial, even an offering made by fire unto Jehovah.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Every sabbath day he shall set it in order before Jehovah continually; it is on the behalf of the children of Israel, an everlasting covenant.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
And it shall be for Aaron and his sons; and they shall eat it in a holy place: for it is most holy unto him of the offerings of Jehovah made by fire by a perpetual statute.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
And the son of an Israelitish woman, whose father was an Egyptian, went out among the children of Israel; and the son of the Israelitish woman and a man of Israel strove together in the camp:
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
and the son of the Israelitish woman blasphemed the Name, and cursed; and they brought him unto Moses. And his mother’s name was Shelomith, the daughter of Dibri, of the tribe of Dan.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
And they put him in ward, that it might be declared unto them at the mouth of Jehovah.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spake unto Moses, saying,
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Bring forth him that hath cursed without the camp; and let all that heard him lay their hands upon his head, and let all the congregation stone him.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
And thou shalt speak unto the children of Israel, saying, Whosoever curseth his God shall bear his sin.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
And he that blasphemeth the name of Jehovah, he shall surely be put to death; all the congregation shall certainly stone him: as well the sojourner, as the home-born, when he blasphemeth the name [of Jehovah], shall be put to death.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And he that smiteth any man mortally shall surely be put to death.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
And he that smiteth a beast mortally shall make it good, life for life.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
And if a man cause a blemish in his neighbor; as he hath done, so shall it be done to him:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
breach for breach, eye for eye, tooth for tooth; as he hath caused a blemish in a man, so shall it be rendered unto him.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
And he that killeth a beast shall make it good: and he that killeth a man shall be put to death.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Ye shall have one manner of law, as well for the sojourner, as for the home-born: for I am Jehovah your God.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And Moses spake to the children of Israel; and they brought forth him that had cursed out of the camp, and stoned him with stones. And the children of Israel did as Jehovah commanded Moses.

< Firistoci 24 >