< Firistoci 24 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Byd Israeliterne at skaffe dig ren Olivenolie af knuste Frugter til Lysestagen, saa Lamperne daglig kan sættes paa.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
I Aabenbaringsteltet uden for Forhænget foran Vidnesbyrdet skal Aron gøre den i Stand, saa den bestandig kan brænde fra Aften til Morgen for HERRENS Aasyn. Det skal være eder en evig gyldig Anordning fra Slægt til Slægt;
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
paa Guldlysestagen skal han holde Lamperne i Orden for HERRENS Aasyn, saa de kan brænde bestandig.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
Du skal tage fint Hvedemel og bage tolv Kager, to Tiendedele Efa til hver Kage,
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
og lægge dem i to Rækker, seks i hver Række, paa Guldbordet for HERRENS Aasyn;
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
paa hver Række skal du lægge ren Røgelse, og den skal være Brødenes Offerdel, et Ildoffer for HERREN.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Han skal bestandig hver Sabbatsdag lægge dem frem for HERRENS Aasyn; det skal være Israeliterne en evig Pagtspligt.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
De skal tilfalde Aron og hans Sønner, som skal spise dem paa et helligt Sted, thi de er højhellige; ham tilfalder de som en evig, retmæssig Del af HERRENS Ildofre.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
En israelitisk Kvindes Søn, hvis Fader var Ægypter, gik ud blandt Israeliterne. Da opstod der Strid i Lejren mellem den israelitiske Kvindes Søn og en Israelit,
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
og den israelitiske Kvindes Søn forbandede Navnet og bespottede det. Da førte man ham til Moses. Hans Moder hed Sjelomit, en Datter af Dibri af Dans Stamme.
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
Og de satte ham i Varetægt for at faa en Kendelse af HERRENS Mund.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Og HERREN talede til Moses og sagde:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Før Spotteren uden for Lejren, og alle de, der hørte det, skal lægge deres Hænder paa hans Hoved, og derefter skal hele Menigheden stene ham.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Og du skal tale til Israeliterne og sige: Naar nogen bespotter sin Gud, skal han undgælde for sin Synd;
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
og den, der forbander HERRENS Navn, skal lide Døden; hele Menigheden skal stene ham; en fremmed saavel som en indfødt skal lide Døden naar han forbander Navnet.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Naar nogen slaar et Menneske ihjel, skal han lide Døden.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Den, der slaar et Stykke Kvæg ihjel, skal erstatte det et levende Dyr for et levende Dyr.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Naar nogen tilføjer sin Næste Legemsskade, skal der handles med ham, som han har handlet,
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
Brud for Brud, Øje for Øje, Tand for Tand; samme Skade, han tilføjer en anden, skal tilføjes ham selv.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Den, der slaar et Stykke Kvæg ihjel, skal erstatte det; men den, der slaar et Menneske ihjel, skal lide Døden.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
En og samme Ret skal gælde for eder; for den fremmede saavel som for den indfødte; thi jeg er HERREN eders Gud!
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Og Moses sagde det til Israeliterne, og de førte Spotteren uden for Lejren og stenede ham; Israeliterne gjorde som HERREN havde paalagt Moses.