< Firistoci 24 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Mluvil pak Hospodin k Mojžíšovi, řka:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
Přikaž synům Izraelským, ať přinesou tobě oleje olivového, čistého, vytlačeného, k svícení, aby lampy ustavičně rozsvěcovány byly.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Před oponou svědectví v stánku úmluvy zpořádá je Aron, aby hořely od večera až do jitra před Hospodinem vždycky. Toť bude ustanovení věčné v národech vašich.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Na svícen čistý rozstavovati bude lampy před Hospodinem vždycky.
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
A vezma mouky bělné, upečeš z ní dvanácte koláčů; jeden každý koláč bude ze dvou desetin efi.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
A rozkladeš je dvěma řady, šest v řadu jednom, na stole čistém před Hospodinem.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
Dáš také na každý řad kadidla čistého, aby bylo za každý chléb ten kouření pamětné v obět ohnivou Hospodinu.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Každého dne sobotního klásti budete je řadem před Hospodinem vždycky, berouce je od synů Izraelských smlouvou věčnou.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
I budou Aronovi a synům jeho, kteřížto jísti budou je na místě svatém; nebo nejsvětější věc jest jim z obětí ohnivých Hospodinových právem věčným.
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
Vyšel pak syn ženy Izraelské, kteréhož měla s mužem Egyptským, mezi syny Izraelskými, a vadili se v staních syn ženy té Izraelské s mužem Izraelským.
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
I zlořečil syn ženy té Izraelské a rouhal se jménu Božímu. Tedy přivedli ho k Mojžíšovi. (Jméno pak matky jeho bylo Salumit, dcera Dabri, z pokolení Dan.)
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
A dali jej do vězení, až by jim bylo oznámeno, co s ním Bůh káže učiniti.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Mluvil pak Hospodin k Mojžíšovi, řka:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
Vyveď toho ruhače ven z stanů, a nechať všickni ti, kteříž slyšeli, vloží ruce na hlavu jeho, a všecken lid ať ho ukamenuje.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Mluvě pak k synům Izraelským, díš jim: Kdož by koli zlořečil Bohu svému, poneseť hřích svůj.
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
Kdož by zlořečil jménu Hospodinovu, smrtí umře, a všecko shromáždění bez milosti ukamenuje jej. Tak cizí, jako doma zchovaný, když by zlořečil jménu Hospodinovu, smrtí umře.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Zabil-li by kdo kterého člověka, smrtí umře.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Jestliže by pak zabil hovado, navrátí jiné, hovado za hovado.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Kdož by pak zohavil bližního svého, vedlé toho, jakž on učinil, tak se staň jemu:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
Zlámaní za zlámaní, oko za oko, zub za zub. Jakouž by ohavu učinil na těle člověka, taková zase učiněna bude jemu.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Kdož by zabil hovado, navrátí jiné, ale kdož by zabil člověka, umře.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Jednostejné právo míti budete. Jakož příchozímu, tak domácímu stane se; nebo já jsem Hospodin Bůh váš.
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Tedy mluvil Mojžíš k synům Izraelským ty věci. I vyvedli toho ruhače ven za stany, a kamením ho zametali. Učinili, pravím, synové Izraelští vedlé toho, jakož přikázal Hospodin Mojžíšovi.

< Firistoci 24 >