< Firistoci 24 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Jahve reče Mojsiju:
2 “Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
“Naredi Izraelcima da ti za svijećnjak donose čistoga ulja od istupanih maslina, da se uvijek održava svjetlo.
3 Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
Neka ga Aron svagda sprema pred Jahvom od večeri do jutra u Šatoru sastanka, pred zavjesom Svjedočanstva. Neka je ovo trajan zakon vašim naraštajima.
4 Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
Neka Aron neprekidno održava svjetlila na čistome svijećnjaku pred Jahvom.”
5 “Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
“Potom uzmi najboljeg brašna i od njega ispeci dvanaest pogača. Neka u svakoj pogači budu dvije desetine efe.
6 A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
Onda ih poredaj u dva reda - po šest u redu - na čistome stolu što je pred Jahvom.
7 Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
Na svaki red stavi čistoga tamjana. Neka to bude hrana prinesena kao spomen - paljena žrtva Jahvi.
8 Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
Svake subote, bez prijekida, neka se postavljaju pred Jahvu. To neka Izraelci vrše zbog vječnoga Saveza.
9 Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
Neka pripadnu Aronu i njegovim sinovima. Oni ih imaju blagovati na posvećenu mjestu. To je njemu vrlo svet dio Jahvinih paljenih žrtava. To neka bude trajna odredba.”
10 To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
A sin jedne Izraelke, komu otac bijaše Egipćanin, iziđe među Izraelce i zametne u taboru svađu s nekim Izraelcem.
11 Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
Uto sin Izraelke pogrdi Ime i opsuje ga. Tada ga dovedu Mojsiju. - Mati mu se zvala Šelomit, a bila je kći Dibrijeva iz plemena Danova. -
12 Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
Stave ga u zatvor dok im se ne očituje volja Jahvina.
13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
Onda Jahve reče Mojsiju:
14 “Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
“Izvedi psovača iz tabora. Potom svi oni koji su ga čuli neka stave svoje ruke na njegovu glavu. A onda neka ga sva zajednica kamenuje.
15 Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
Poslije toga ćeš ovako prozboriti Izraelcima: Tko god opsuje Boga svoga neka snosi svoju krivnju;
16 duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
tko izgovori hulu na ime Jahvino neka se smakne - neka ga sva zajednica kamenuje; bio stranac ili domorodac, ako pohuli ime Jahvino, mora mrijeti.
17 “‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Ako čovjek zada smrtan udarac drugome, mora se smaknuti.
18 Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
Tko usmrti živinče mora ga nadomjestiti: život za život.
19 Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
Tko ozlijedi svoga bližnjega neka mu se učini kako je on učinio:
20 karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
lom za lom, oko za oko, zub za zub - rana koju je on zadao drugome neka se zada i njemu.
21 Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
Tko usmrti živinče mora ga nadoknaditi, ali tko ubije čovjeka mora umrijeti.
22 Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Neka vam je jednak sud i strancu i domorocu. Jer ja sam Jahve, Bog vaš.”
23 Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Pošto je Mojsije to izložio Izraelcima, oni izvedu psovača izvan tabora i zaspu ga kamenjem. Učine, dakle, Izraelci kako je Jahve Mojsiju naredio.