< Firistoci 23 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
2 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga ƙayyadaddun bukukkuwa, ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji, da za ku sanar wa mutane su riƙa kiyayewa, su zama lokutan tarurruka masu tsarki.
Speak to the children of Israel, and say to them, [Concerning] the feasts of the LORD, which ye shall proclaim [to be] holy convocations, [even] these [are] my feasts.
3 “‘Akwai kwanaki shida da za ku iya yin aiki, amma rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, rana mai tsarki ga jama’a. Kada ku yi wani aiki a ko’ina kuke da zama, Asabbaci ne ga Ubangiji.
Six days shall work be done: but the seventh day [is] the sabbath of rest, a holy convocation: ye shall do no work [in it]: it [is] the sabbath of the LORD in all your dwellings.
4 “‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa da tsarkakakkun taron jama’a za su yi a ƙayyadaddun lokuta.
These [are] the feasts of the LORD, holy convocations, which ye shall proclaim in their seasons.
5 Bikin Ƙetarewar Ubangiji, zai fara da yamma a ranar goma sha huɗu na wata na fari.
In the fourteenth [day] of the first month at evening [is] the LORD'S passover.
6 A rana ta goma sha biyar na wannan wata, za a fara Bikin Burodi Marar Yisti na Ubangiji. Za ku yi kwana bakwai kuna cin burodi marar yisti.
And on the fifteenth day of the same month [is] the feast of unleavened bread to the LORD, seven days ye must eat unleavened bread.
7 A rana ta fari, ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba.
In the first day ye shall have a holy convocation: ye shall do no servile work in it.
8 Kwana bakwai za ku miƙa hadaya ga Ubangiji da wuta. A rana ta bakwai ɗin ku yi taro mai tsarki, ba za ku kuwa yi aiki na kullum ba.’”
But ye shall offer an offering made by fire to the LORD seven days: in the seventh day [is] a holy convocation, ye shall do no servile work [in it].
9 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
10 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, kuka kuma girbe amfanin gonarta, sai ku kawo wa firist damin hatsi na farko da kuka girbe.
Speak to the children of Israel, and say to them, When ye shall have come into the land which I give to you, and shall reap the harvest thereof, then ye shall bring a sheaf of the first-fruits of your harvest to the priest:
11 Zai kaɗa damin a gaban Ubangiji domin yă zama yardajje a madadinku; firist ɗin zai kaɗa shi a kashegarin Asabbaci.
And he shall wave the sheaf before the LORD, to be accepted for you: on the morrow after the sabbath the priest shall wave it.
12 A ranar da kuka kaɗa damin, dole ku miƙa hadaya ta ƙonawa na ɗan rago bana ɗaya, marar lahani ga Ubangiji,
And ye shall offer, that day when ye wave the sheaf, a he-lamb without blemish of the first year for a burnt-offering to the LORD.
13 tare da hadaya ta gari mai laushi, humushi biyu haɗe da mai, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, da kuma abin sha kwalaba ɗaya na ruwan inabi.
And the meat-offering thereof [shall be] two tenth-parts of fine flour mingled with oil, an offering made by fire to the LORD [for] a sweet savor: and the drink-offering thereof [shall be] of wine, the fourth [part] of a hin.
14 Ba za ku ci wani burodi, ko gasasshen hatsi, ko sabon hatsi ba, sai ran nan da kuka kawo wannan hadaya ga Allahnku. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a duk inda kuke zama.
And ye shall eat neither bread, nor parched corn, nor green ears, until the same day that ye have brought an offering to your God: [It shall be] a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
15 “‘Daga kashegarin Asabbaci, ranar da kuka kawo dami don hadaya ta kaɗawa, ku ƙirga cikakku makoni bakwai.
And ye shall count to you from the morrow after the sabbath, from the day that ye brought the sheaf of the wave-offering; seven sabbaths shall be complete:
16 Ku ƙirga kwana hamsin har zuwa kashegarin Asabbaci na bakwai, sa’an nan ku miƙa hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji.
Even to the morrow after the seventh sabbath shall ye number fifty days; and ye shall offer a new meat-offering to the LORD.
17 Daga ko’ina kuke da zama, ku kawo dunƙule biyu na humushin gari mai laushi da aka tuya da yisti, a matsayin hadaya ta kaɗawa ta’ya’yan fari na itatuwa ga Ubangiji.
Ye shall bring out of your habitations two wave-loaves of two tenth-parts: they shall be of fine flour, they shall be baked with leaven, [they are] the first-fruits to the LORD.
18 Tare da wannan, ku miƙa’yan raguna bakwai, kowanne bana ɗaya-ɗaya marar lahani, bijimi da kuma raguna biyu. Za su zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, tare da hadayunsu na hatsi, da hadayunsu na sha, hadaya da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
And ye shall offer with the bread seven lambs without blemish of the first year, and one young bullock, and two rams: they shall be [for] a burnt-offering to the LORD, with their meat-offering, and their drink offerings, [even] an offering made by fire of a sweet savor to the LORD.
19 Sa’an nan ku miƙa bunsuru ɗaya na hadaya don zunubi, da’yan raguna biyu, kowanne bana ɗaya-ɗaya, don hadaya ta salama.
Then ye shall sacrifice one kid of the goats for a sin-offering, and two lambs of the first year for a sacrifice of peace-offerings.
20 Firist zai kaɗa’yan raguna biyun a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, tare da burodin sababbin’ya’yan fari na itatuwan. Tsarkaken hadaya ce ga Ubangiji ga firist.
And the priest shall wave them with the bread of the first-fruits [for] a wave-offering before the LORD, with the two lambs: they shall be holy to the LORD for the priest.
21 A wannan rana za ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
And ye shall proclaim on the same day, [that] it may be a holy convocation to you: ye shall do no servile work [in it]. [it shall be] a statute for ever in all your dwellings throughout your generations.
22 “‘Sa’ad da kuka yi girbin gonarku, kada ku girbe har ƙarshen gefen gonar, ko ku yi kalar girbinku. Ku bar su wa matalauta da baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
And when ye reap the harvest of your land, thou shalt not make clean riddance of the corners of thy field when thou reapest, neither shalt thou gather any gleaning of thy harvest: thou shalt leave them to the poor, and to the stranger: I [am] the LORD your God.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
24 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar farko ga wata na bakwai, za tă zama ranar hutu, rana ce ta tuni da yin taro mai tsarki na sujada da za a fara busar ƙaho.
Speak to the children of Israel, saying, In the seventh month, in the first [day] of the month, shall ye have a sabbath, a memorial of blowing of trumpets, a holy convocation.
25 Kada ku yi aiki na kullum, amma ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.’”
Ye shall do no servile work [in it]; but ye shall offer an offering made by fire to the LORD.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
27 “Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.
Also on the tenth [day] of this seventh month [there shall be] a day of atonement; it shall be a holy convocation to you, and ye shall afflict your souls, and offer an offering made by fire to the LORD.
28 Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.
And ye shall do no work in that same day; for it [is] a day of atonement, to make an atonement for you before the LORD your God.
29 Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.
For whatever soul [it may be] that shall not be afflicted in that same day, he shall be cut off from among his people.
30 Zan hallaka duk wani da ya yi aiki a wannan rana daga mutanensa.
And whatever soul [it may be] that doeth any work in that same day, the same soul will I destroy from among his people.
31 Sam ba za ku yi wani aiki ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce, wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
Ye shall do no manner of work. [It shall be] a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
32 Asabbaci ne na hutu dominku, kuma dole ku yi mūsun kanku. Daga yamman rana ta tara ga wata, har zuwa yamma na biye, za ku kiyaye Asabbacinku.”
It [shall be] to you a sabbath of rest, and ye shall afflict your souls in the ninth [day] of the month at evening: from evening to evening shall ye celebrate your sabbath.
33 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
34 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, za a fara Bikin Tabanakul na Ubangiji, zai kuma ɗauki kwana bakwai.
Speak to the children of Israel, saying, The fifteenth day of this seventh month [shall be] the feast of tabernacles [for] seven days to the LORD.
35 A ranar farko za tă zama ta taro mai tsarki, kada ku yi aiki na kullum.
On the first day [shall be] a holy convocation: ye shall do no servile work [in it].
36 Kwana bakwai za ku miƙa hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, a rana ta takwas, ku yi taro mai tsarki, ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji. Wannan ranar rufewar taro ce; kada ku yi aiki na kullum.
Seven days ye shall offer an offering made by fire to the LORD: on the eighth day shall be a holy convocation to you, and ye shall offer an offering made by fire to the LORD: it [is] a solemn assembly; [and] ye shall do no servile work [in it].
37 (“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa, waɗanda za ku yi a matsayin tsarkakakkun taro, don kawo hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, hadayu na ƙonawa da hadayu na hatsi, sadaka da kuma hadayu na sha, da ake bukata kowace rana.
These [are] the feasts of the LORD, which ye shall proclaim [to be] holy convocations, to offer an offering made by fire to the LORD, a burnt-offering, and a meat-offering, a sacrifice, and drink-offerings, every thing upon its day:
38 Waɗannan hadayu, ƙari ne a kan waɗannan na Asabbatan Ubangiji, haɗe kuma da kyautanku, da kome da kuka yi alkawari, da kuma hadayu yardar ran da za ku ba wa Ubangiji.)
Beside the sabbaths of the LORD, and beside your gifts, and beside all your vows, and beside all your free-will-offerings, which ye give to the LORD.
39 “‘Saboda haka, farawa daga ranar goma sha biyar ga watan bakwai, bayan kun tara hatsin gona, ku yi bikin Ubangiji kwana bakwai; rana ta fari, rana hutu ce, rana ta takwas kuma rana hutu ce.
Also in the fifteenth day of the seventh month, when ye have gathered in the fruit of the land, ye shall keep a feast to the LORD seven days: on the first day [shall be] a sabbath, and on the eighth day [shall be] a sabbath.
40 A rana ta fari, za ku ɗebi zaɓaɓɓun’ya’yan itatuwa daga itatuwa, da rassan dabino, rassa masu ganye, da kuma ganyayen itacen wardi na rafi, ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, kwana bakwai.
And ye shall take you on the first day the boughs of goodly trees, branches of palm-trees, and the boughs of thick trees, and willows of the brook; and ye shall rejoice before the LORD your God seven days.
41 Za ku kiyaye bikin nan har kwana bakwai a kowace shekara ga Ubangiji. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsarraraki masu zuwa, ku kiyaye ta a wata na bakwai.
And ye shall keep it a feast to the LORD seven days in the year. [It shall be] a statute for ever in your generations; ye shall celebrate it in the seventh month.
42 Ku zauna a bukkoki kwana bakwai. Dukan’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa, za su zauna a bukkoki
Ye shall dwell in booths seven days: all that are Israelites born shall dwell in booths:
43 don zuriyarku tă san cewa na sa Isra’ilawa suka zauna a bukkoki sa’ad da na fitar da su daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
That your generations may know that I made the children of Israel to dwell in booths, when I brought them out of the land of Egypt: I [am] the LORD your God.
44 Saboda haka Musa ya sanar wa Isra’ilawa ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji.
And Moses declared to the children of Israel the feasts of the LORD.

< Firistoci 23 >