< Firistoci 23 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
2 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga ƙayyadaddun bukukkuwa, ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji, da za ku sanar wa mutane su riƙa kiyayewa, su zama lokutan tarurruka masu tsarki.
Speak unto the children of Israel, and say unto them, The set feasts of the LORD, which ye shall proclaim to be holy convocations, even these are my set feasts.
3 “‘Akwai kwanaki shida da za ku iya yin aiki, amma rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, rana mai tsarki ga jama’a. Kada ku yi wani aiki a ko’ina kuke da zama, Asabbaci ne ga Ubangiji.
Six days shall work be done: but on the seventh day is a sabbath of solemn rest, an holy convocation; ye shall do no manner of work: it is a sabbath unto the LORD in all your dwellings.
4 “‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa da tsarkakakkun taron jama’a za su yi a ƙayyadaddun lokuta.
These are the set feasts of the LORD, even holy convocations, which ye shall proclaim in their appointed season.
5 Bikin Ƙetarewar Ubangiji, zai fara da yamma a ranar goma sha huɗu na wata na fari.
In the first month, on the fourteenth day of the month at even, is the LORD’S passover.
6 A rana ta goma sha biyar na wannan wata, za a fara Bikin Burodi Marar Yisti na Ubangiji. Za ku yi kwana bakwai kuna cin burodi marar yisti.
And on the fifteenth day of the same month is the feast of unleavened bread unto the LORD: seven days ye shall eat unleavened bread.
7 A rana ta fari, ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba.
In the first day ye shall have an holy convocation: ye shall do no servile work.
8 Kwana bakwai za ku miƙa hadaya ga Ubangiji da wuta. A rana ta bakwai ɗin ku yi taro mai tsarki, ba za ku kuwa yi aiki na kullum ba.’”
But ye shall offer an offering made by fire unto the LORD seven days: in the seventh day is an holy convocation; ye shall do no servile work.
9 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
10 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, kuka kuma girbe amfanin gonarta, sai ku kawo wa firist damin hatsi na farko da kuka girbe.
Speak unto the children of Israel, and say unto them, When ye be come into the land which I give unto you, and shall reap the harvest thereof, then ye shall bring the sheaf of the firstfruits of your harvest unto the priest:
11 Zai kaɗa damin a gaban Ubangiji domin yă zama yardajje a madadinku; firist ɗin zai kaɗa shi a kashegarin Asabbaci.
and he shall wave the sheaf before the LORD, to be accepted for you: on the morrow after the sabbath the priest shall wave it.
12 A ranar da kuka kaɗa damin, dole ku miƙa hadaya ta ƙonawa na ɗan rago bana ɗaya, marar lahani ga Ubangiji,
And in the day when ye wave the sheaf, ye shall offer a he-lamb without blemish of the first year for a burnt offering unto the LORD.
13 tare da hadaya ta gari mai laushi, humushi biyu haɗe da mai, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, da kuma abin sha kwalaba ɗaya na ruwan inabi.
And the meal offering thereof shall be two tenth parts [of an ephah] of fine flour mingled with oil, an offering made by fire unto the LORD for a sweet savour: and the drink offering thereof shall be of wine, the fourth part of an hin.
14 Ba za ku ci wani burodi, ko gasasshen hatsi, ko sabon hatsi ba, sai ran nan da kuka kawo wannan hadaya ga Allahnku. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a duk inda kuke zama.
And ye shall eat neither bread, nor parched corn, nor fresh ears, until this selfsame day, until ye have brought the oblation of your God: it is a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
15 “‘Daga kashegarin Asabbaci, ranar da kuka kawo dami don hadaya ta kaɗawa, ku ƙirga cikakku makoni bakwai.
And ye shall count unto you from the morrow after the sabbath, from the day that ye brought the sheaf of the wave offering; seven sabbaths shall there be complete:
16 Ku ƙirga kwana hamsin har zuwa kashegarin Asabbaci na bakwai, sa’an nan ku miƙa hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji.
even unto the morrow after the seventh sabbath shall ye number fifty days; and ye shall offer a new meal offering unto the LORD.
17 Daga ko’ina kuke da zama, ku kawo dunƙule biyu na humushin gari mai laushi da aka tuya da yisti, a matsayin hadaya ta kaɗawa ta’ya’yan fari na itatuwa ga Ubangiji.
Ye shall bring out of your habitations two wave loaves of two tenth parts [of an ephah]: they shall be of fine flour, they shall be baken with leaven, for firstfruits unto the LORD.
18 Tare da wannan, ku miƙa’yan raguna bakwai, kowanne bana ɗaya-ɗaya marar lahani, bijimi da kuma raguna biyu. Za su zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, tare da hadayunsu na hatsi, da hadayunsu na sha, hadaya da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
And ye shall present with the bread seven lambs without blemish of the first year, and one young bullock, and two rams: they shall be a burnt offering unto the LORD, with their meal offering, and their drink offerings, even an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.
19 Sa’an nan ku miƙa bunsuru ɗaya na hadaya don zunubi, da’yan raguna biyu, kowanne bana ɗaya-ɗaya, don hadaya ta salama.
And ye shall offer one he-goat for a sin offering, and two he-lambs of the first year for a sacrifice of peace offerings.
20 Firist zai kaɗa’yan raguna biyun a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, tare da burodin sababbin’ya’yan fari na itatuwan. Tsarkaken hadaya ce ga Ubangiji ga firist.
And the priest shall wave them with the bread of the firstfruits for a wave offering before the LORD, with the two lambs: they shall be holy to the LORD for the priest.
21 A wannan rana za ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
And ye shall make proclamation on the selfsame day; there shall be an holy convocation unto you: ye shall do no servile work: it is a statute for ever in all your dwellings throughout your generations.
22 “‘Sa’ad da kuka yi girbin gonarku, kada ku girbe har ƙarshen gefen gonar, ko ku yi kalar girbinku. Ku bar su wa matalauta da baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
And when ye reap the harvest of your land, thou shalt not wholly reap the corners of thy field, neither shalt thou gather the gleaning of thy harvest: thou shalt leave them for the poor, and for the stranger: I am the LORD your God.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
24 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar farko ga wata na bakwai, za tă zama ranar hutu, rana ce ta tuni da yin taro mai tsarki na sujada da za a fara busar ƙaho.
Speak unto the children of Israel, saying, In the seventh month, in the first day of the month, shall be a solemn rest unto you, a memorial of blowing of trumpets, an holy convocation.
25 Kada ku yi aiki na kullum, amma ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.’”
Ye shall do no servile work: and ye shall offer an offering made by fire unto the LORD.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
27 “Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.
Howbeit on the tenth day of this seventh month is the day of atonement: it shall be an holy convocation unto you, and ye shall afflict your souls; and ye shall offer an offering made by fire unto the LORD.
28 Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.
And ye shall do no manner of work in that same day: for it is a day of atonement, to make atonement for you before the LORD your God.
29 Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.
For whatsoever soul it be that shall not be afflicted in that same day, he shall be cut off from his people.
30 Zan hallaka duk wani da ya yi aiki a wannan rana daga mutanensa.
And whatsoever soul it be that doeth any manner of work in that same day, that soul will I destroy from among his people.
31 Sam ba za ku yi wani aiki ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce, wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
Ye shall do no manner of work: it is a statute for ever throughout your generations in all your dwellings.
32 Asabbaci ne na hutu dominku, kuma dole ku yi mūsun kanku. Daga yamman rana ta tara ga wata, har zuwa yamma na biye, za ku kiyaye Asabbacinku.”
It shall be unto you a sabbath of solemn rest, and ye shall afflict your souls: in the ninth day of the month at even, from even unto even, shall ye keep your sabbath.
33 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses, saying,
34 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, za a fara Bikin Tabanakul na Ubangiji, zai kuma ɗauki kwana bakwai.
Speak unto the children of Israel, saying, On the fifteenth day of this seventh month is the feast of tabernacles for seven days unto the LORD.
35 A ranar farko za tă zama ta taro mai tsarki, kada ku yi aiki na kullum.
On the first day shall be an holy convocation: ye shall do no servile work.
36 Kwana bakwai za ku miƙa hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, a rana ta takwas, ku yi taro mai tsarki, ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji. Wannan ranar rufewar taro ce; kada ku yi aiki na kullum.
Seven days ye shall offer an offering made by fire unto the LORD: on the eighth day shall be an holy convocation unto you; and ye shall offer an offering made by fire unto the LORD: it is a solemn assembly; ye shall do no servile work.
37 (“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa, waɗanda za ku yi a matsayin tsarkakakkun taro, don kawo hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, hadayu na ƙonawa da hadayu na hatsi, sadaka da kuma hadayu na sha, da ake bukata kowace rana.
These are the set feasts of the LORD, which ye shall proclaim to be holy convocations, to offer an offering made by fire unto the LORD, a burnt offering, and a meal offering, a sacrifice, and drink offerings, each on its own day:
38 Waɗannan hadayu, ƙari ne a kan waɗannan na Asabbatan Ubangiji, haɗe kuma da kyautanku, da kome da kuka yi alkawari, da kuma hadayu yardar ran da za ku ba wa Ubangiji.)
beside the sabbaths of the LORD, and beside your gifts, and beside all your vows, and beside all your freewill offerings, which ye give unto the LORD.
39 “‘Saboda haka, farawa daga ranar goma sha biyar ga watan bakwai, bayan kun tara hatsin gona, ku yi bikin Ubangiji kwana bakwai; rana ta fari, rana hutu ce, rana ta takwas kuma rana hutu ce.
Howbeit on the fifteenth day of the seventh month, when ye have gathered in the fruits of the land, ye shall keep the feast of the LORD seven days: on the first day shall be a solemn rest, and on the eighth day shall be a solemn rest.
40 A rana ta fari, za ku ɗebi zaɓaɓɓun’ya’yan itatuwa daga itatuwa, da rassan dabino, rassa masu ganye, da kuma ganyayen itacen wardi na rafi, ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, kwana bakwai.
And ye shall take you on the first day the fruit of goodly trees, branches of palm trees, and boughs of thick trees, and willows of the brook; and ye shall rejoice before the LORD your God seven days.
41 Za ku kiyaye bikin nan har kwana bakwai a kowace shekara ga Ubangiji. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsarraraki masu zuwa, ku kiyaye ta a wata na bakwai.
And ye shall keep it a feast unto the LORD seven days in the year: it is a statute for ever in your generations: ye shall keep it in the seventh month.
42 Ku zauna a bukkoki kwana bakwai. Dukan’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa, za su zauna a bukkoki
Ye shall dwell in booths seven days; all that are homeborn in Israel shall dwell in booths:
43 don zuriyarku tă san cewa na sa Isra’ilawa suka zauna a bukkoki sa’ad da na fitar da su daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
that your generations may know that I made the children of Israel to dwell in booths, when I brought them out of the land of Egypt: I am the LORD your God.
44 Saboda haka Musa ya sanar wa Isra’ilawa ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji.
And Moses declared unto the children of Israel the set feasts of the LORD.