< Firistoci 23 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede til Mose og sagde:
2 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga ƙayyadaddun bukukkuwa, ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji, da za ku sanar wa mutane su riƙa kiyayewa, su zama lokutan tarurruka masu tsarki.
Tal til Israels Børn og sig til dem: Hvad angaar Herrens bestemte Tider, som I skulle udraabe som hellige Sammenkaldelser, da ere disse mine bestemte Tider.
3 “‘Akwai kwanaki shida da za ku iya yin aiki, amma rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, rana mai tsarki ga jama’a. Kada ku yi wani aiki a ko’ina kuke da zama, Asabbaci ne ga Ubangiji.
Seks Dage skal al Gerning gøres, men paa den syvende Dag er en Hviles Sabbat, en hellig Sammenkaldelse, da skulle I ingen Gerning gøre, den er for Herren en Sabbat i alle eders Boliger.
4 “‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa da tsarkakakkun taron jama’a za su yi a ƙayyadaddun lokuta.
Disse ere Herrens bestemte Tider, de hellige Sammenkaldelser, som I skulle udraabe til deres bestemte Tider.
5 Bikin Ƙetarewar Ubangiji, zai fara da yamma a ranar goma sha huɗu na wata na fari.
I den første Maaned, paa den fjortende Dag i Maaneden, mellem de tvende Aftener, da er det Paaske for Herren.
6 A rana ta goma sha biyar na wannan wata, za a fara Bikin Burodi Marar Yisti na Ubangiji. Za ku yi kwana bakwai kuna cin burodi marar yisti.
Og paa den femtende Dag i denne Maaned er de usyrede Brøds Højtid for Herren; I skulle æde usyrede Brød i syv Dage.
7 A rana ta fari, ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba.
Paa den første Dag skal være eder en hellig Sammenkaldelse, da skulle I ingen Arbejdsgerning gøre.
8 Kwana bakwai za ku miƙa hadaya ga Ubangiji da wuta. A rana ta bakwai ɗin ku yi taro mai tsarki, ba za ku kuwa yi aiki na kullum ba.’”
Og I skulle ofre Ildofre for Herren i syv Dage; paa den syvende Dag skal være en hellig Sammenkaldelse, I skulle ikke gøre nogen Arbejdsgerning.
9 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede til Mose og sagde:
10 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, kuka kuma girbe amfanin gonarta, sai ku kawo wa firist damin hatsi na farko da kuka girbe.
Tal til Israels Børn og sig til dem: Naar I komme ind i det Land, som jeg vil give eder, og I høste dets Høst, da skulle I fremføre et Neg af det første af eders Høst til Præsten.
11 Zai kaɗa damin a gaban Ubangiji domin yă zama yardajje a madadinku; firist ɗin zai kaɗa shi a kashegarin Asabbaci.
Og han skal røre Neget for Herrens Ansigt, for eder til en Behagelighed; den anden Dag efter Sabbaten skal Præsten røre det.
12 A ranar da kuka kaɗa damin, dole ku miƙa hadaya ta ƙonawa na ɗan rago bana ɗaya, marar lahani ga Ubangiji,
Og I skulle gøre Offer paa den samme Dag, naar I røre Neget, et Lam uden Lyde, aargammelt, til et Brændoffer for Herren,
13 tare da hadaya ta gari mai laushi, humushi biyu haɗe da mai, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, da kuma abin sha kwalaba ɗaya na ruwan inabi.
og dets Madoffer, to Tiendeparter Mel blandet med Olie til et Ildoffer for Herren, til en behagelig Lugt; og dets Drikoffer af Vin, en Fjerdepart af en Hin.
14 Ba za ku ci wani burodi, ko gasasshen hatsi, ko sabon hatsi ba, sai ran nan da kuka kawo wannan hadaya ga Allahnku. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a duk inda kuke zama.
Og I skulle ikke æde Brød eller ristede Aks eller Korn indtil den Dag, indtil I føre eders Guds Offer frem; dette skal være hos eders Efterkommere en evig Skik i alle eders Boliger.
15 “‘Daga kashegarin Asabbaci, ranar da kuka kawo dami don hadaya ta kaɗawa, ku ƙirga cikakku makoni bakwai.
Og I skulle tælle eder fra anden Dagen efter den Sabbat, fra den Dag I bære Rørelsens Neg frem; syv hele Uger skulle de være;
16 Ku ƙirga kwana hamsin har zuwa kashegarin Asabbaci na bakwai, sa’an nan ku miƙa hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji.
til Dagen efter den syvende Uge skulle I tælle halvtredsindstyve Dage: Saa skulle I ofre nyt Madoffer for Herren.
17 Daga ko’ina kuke da zama, ku kawo dunƙule biyu na humushin gari mai laushi da aka tuya da yisti, a matsayin hadaya ta kaɗawa ta’ya’yan fari na itatuwa ga Ubangiji.
Af eders Boliger skulle I frembære Rørelsens Brød, der skal være to Brød af to Tiendeparter Mel, med Surdejg skulle de bages; de ere en Førstegrøde for Herren.
18 Tare da wannan, ku miƙa’yan raguna bakwai, kowanne bana ɗaya-ɗaya marar lahani, bijimi da kuma raguna biyu. Za su zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, tare da hadayunsu na hatsi, da hadayunsu na sha, hadaya da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Og I skulle ofre tillige med Brødet syv Lam uden Lyde, aargamle, og en Tyrekalv og to Vædre; de skulle være et Brændoffer for Herren, tillige med deres Madoffer og deres Drikoffer, det er en behagelig Lugts Ildoffer for Herren.
19 Sa’an nan ku miƙa bunsuru ɗaya na hadaya don zunubi, da’yan raguna biyu, kowanne bana ɗaya-ɗaya, don hadaya ta salama.
Og I skulle lave een Gedebuk til Syndoffer, og to Lam, aargamle, til Takoffer.
20 Firist zai kaɗa’yan raguna biyun a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, tare da burodin sababbin’ya’yan fari na itatuwan. Tsarkaken hadaya ce ga Ubangiji ga firist.
Og Præsten skal røre dem tillige med Førstegrødens Brød med en Rørelse for Herrens Ansigt, tillige de to Lam; de skulle være helligede Herren og tilhøre Præsten.
21 A wannan rana za ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
Og I skulle kalde sammen paa den Dag, det skal være eder en hellig Sammenkaldelse, I skulle ingen Arbejdsgerning gøre; det skal være en evig Skik i alle eders Boliger hos eders Efterkommere,
22 “‘Sa’ad da kuka yi girbin gonarku, kada ku girbe har ƙarshen gefen gonar, ko ku yi kalar girbinku. Ku bar su wa matalauta da baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Og naar I høste eders Lands Høst, da skal du ikke skære det yderste aldeles op paa din Ager, haar du høster, og ej sanke nøje i din Høst; du skal lade det blive til den fattige og til den fremmede; jeg er Herren eders Gud.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede: til Mose og sagde:
24 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar farko ga wata na bakwai, za tă zama ranar hutu, rana ce ta tuni da yin taro mai tsarki na sujada da za a fara busar ƙaho.
Tal til Israels Børn og sig: I den syvende Maaned, paa den første Dag i Maaneden, skal der være eder en Hvile, en Basunklang til Ihukommelse, en hellig Sammenkaldelse.
25 Kada ku yi aiki na kullum, amma ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.’”
Og I skulle ingen Arbejdsgerning gøre, og I skulle ofre Ildoffer for Herren.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede til Mose og sagde:
27 “Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.
Fremdeles paa den tiende Dag i denne syvende Maaned er det Forligelsens Dag; den skal være eder en hellig Sammenkaldelse, og I skulle ydmyge eders Sjæle, og I skulle ofre Ildoffer for Herren.
28 Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.
Og I skulle ingen Gerning gøre paa den Dag; thi den er Forligelsens Dag, til at gøre Forligelse for eder, for Herren, eders Guds Ansigt.
29 Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.
Thi hver Sjæl, som ikke ydmyger sig paa den samme Dag, den skal udryddes fra sit Folk.
30 Zan hallaka duk wani da ya yi aiki a wannan rana daga mutanensa.
Og hver Sjæl, som gør noget Arbejde paa denne samme Dag, den Sjæl vil jeg ødelægge af hans Folks Midte.
31 Sam ba za ku yi wani aiki ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce, wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
I skulle intet Arbejde gøre; det skal være en evig Skik hos eders Efterkommere i alle eders Boliger.
32 Asabbaci ne na hutu dominku, kuma dole ku yi mūsun kanku. Daga yamman rana ta tara ga wata, har zuwa yamma na biye, za ku kiyaye Asabbacinku.”
Denne er eder en Hviles Sabbat, at I skulle ydmyge eders Sjæle; paa den niende Dag i Maaneden om Aftenen, fra den ene Aften til anden skulle I hvile paa eders Sabbat.
33 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talede til Mose og sagde:
34 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, za a fara Bikin Tabanakul na Ubangiji, zai kuma ɗauki kwana bakwai.
Tal til Israels Børn og sig: Paa den femtende Dag i denne syvende Maaned er Løvsalernes Højtid i syv Dage for Herren.
35 A ranar farko za tă zama ta taro mai tsarki, kada ku yi aiki na kullum.
Paa den første Dag skal være en hellig Sammenkaldelse; I skulle ingen Arbejdsgerning gøre.
36 Kwana bakwai za ku miƙa hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, a rana ta takwas, ku yi taro mai tsarki, ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji. Wannan ranar rufewar taro ce; kada ku yi aiki na kullum.
I skulle ofre Ildoffer for Herren syv Dage; paa den ottende Dag skal der være eder en hellig Sammenkaldelse, og I skulle ofre Herren Ildoffer, det er Slutningshøjtid, I skulle ingen Arbejdsgerning gøre.
37 (“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa, waɗanda za ku yi a matsayin tsarkakakkun taro, don kawo hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, hadayu na ƙonawa da hadayu na hatsi, sadaka da kuma hadayu na sha, da ake bukata kowace rana.
Disse ere Herrens bestemte Tider, som I skulle udraabe som hellige Sammenkaldelser, at ofre for Herren Ildoffer, Brændoffer og Madoffer, Slagtoffer og Drikoffer, hver Dags Gerning paa sin Dag;
38 Waɗannan hadayu, ƙari ne a kan waɗannan na Asabbatan Ubangiji, haɗe kuma da kyautanku, da kome da kuka yi alkawari, da kuma hadayu yardar ran da za ku ba wa Ubangiji.)
foruden Herrens Sabbater og foruden eders Gaver og foruden alle eders Løfter og foruden alle eders frivillige Ofre, som I skulle give Herren.
39 “‘Saboda haka, farawa daga ranar goma sha biyar ga watan bakwai, bayan kun tara hatsin gona, ku yi bikin Ubangiji kwana bakwai; rana ta fari, rana hutu ce, rana ta takwas kuma rana hutu ce.
Men paa den femtende Dag i den syvende Maaned, naar I samle Jordens Grøde, skulle I højtidelig holde Herrens Højtid syv Dage; paa den første Dag skal være en Hvile og paa den ottende Dag skal være en Hvile.
40 A rana ta fari, za ku ɗebi zaɓaɓɓun’ya’yan itatuwa daga itatuwa, da rassan dabino, rassa masu ganye, da kuma ganyayen itacen wardi na rafi, ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, kwana bakwai.
Og I skulle tage eder paa den første Dag Frugt af skønne Træer, Palmekviste og Grene af løvrige Træer og Vidier ved Bække, og I skulle være glade for Herren eders Guds Ansigt syv Dage.
41 Za ku kiyaye bikin nan har kwana bakwai a kowace shekara ga Ubangiji. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsarraraki masu zuwa, ku kiyaye ta a wata na bakwai.
Og I skulle højtidelig holde denne Højtid for Herren syv Dage om Aaret; til en evig Skik hos eders Efterkommere, i den syvende Maaned skulle I højtidelig holde den.
42 Ku zauna a bukkoki kwana bakwai. Dukan’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa, za su zauna a bukkoki
Syv Dage skulle I bo i Hytter, hver indfødt i Israel skal bo i Hytter,
43 don zuriyarku tă san cewa na sa Isra’ilawa suka zauna a bukkoki sa’ad da na fitar da su daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
paa det eders Efterkommere skulle vide, at jeg lod Israels Børn bo i Hytter, der jeg udførte dem af Ægyptens Land; jeg er Herren eders Gud.
44 Saboda haka Musa ya sanar wa Isra’ilawa ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji.
Og Mose talede om Herrens bestemte Tider til Israels Børn.