< Firistoci 23 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
BOEIPA loh Moses te a voek tih,
2 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga ƙayyadaddun bukukkuwa, ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji, da za ku sanar wa mutane su riƙa kiyayewa, su zama lokutan tarurruka masu tsarki.
“Israel ca rhoek te voek lamtah thui pah. BOEIPA kah khoning te hoe uh lamtah ka khoning vaengah a cim tingtunnah te khuehuh.
3 “‘Akwai kwanaki shida da za ku iya yin aiki, amma rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, rana mai tsarki ga jama’a. Kada ku yi wani aiki a ko’ina kuke da zama, Asabbaci ne ga Ubangiji.
Hnin rhuk khuiah bi saii uh saeh. Hnin rhih dongah koiyaeh Sabbath la om saeh lamtah a cim tingtunnah om saeh. BOEIPA kah Sabbath vaengah na tolrhum tom ah bitat khat khaw saii uh boeh.
4 “‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa da tsarkakakkun taron jama’a za su yi a ƙayyadaddun lokuta.
Amah khoning vaengah tahae kah BOEIPA khotue he doek uh lamtah a cim tingtunnah khuehuh.
5 Bikin Ƙetarewar Ubangiji, zai fara da yamma a ranar goma sha huɗu na wata na fari.
Hla lamhma dongkah hlasae hnin hlai li hlaem ah BOEIPA kah Yoom om ni.
6 A rana ta goma sha biyar na wannan wata, za a fara Bikin Burodi Marar Yisti na Ubangiji. Za ku yi kwana bakwai kuna cin burodi marar yisti.
Hlasae hnin hlai nga dongah BOEIPA kah vaidamding khotue om saeh lamtah hnin rhih khuiah vaidamding ca uh.
7 A rana ta fari, ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba.
A cuek khohnin dongah nangmih ham a cim tingtunnah om saeh lamtah thohtatnah bitat boeih tah saii boeh.
8 Kwana bakwai za ku miƙa hadaya ga Ubangiji da wuta. A rana ta bakwai ɗin ku yi taro mai tsarki, ba za ku kuwa yi aiki na kullum ba.’”
Hnin rhih khuiah BOEIPA taengla hmaihlutnah nawn uh. A hnin rhih dongah a cim tingtunnah om saeh lamtah thohtatnah bitat boeih te tah saii uh boeh,” a ti nah.
9 Ubangiji ya ce wa Musa,
Te phoeiah Moses te BOEIPA loh a voek tih,
10 “Yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da zan ba ku, kuka kuma girbe amfanin gonarta, sai ku kawo wa firist damin hatsi na farko da kuka girbe.
“Israel ca rhoek te voek lamtah thui pah. Kai loh nangmih taengah kam paek khohmuen la na kun uh tih cang na ah uh atah na cangah cuek kah canghmuei te khosoih taengla thak uh.
11 Zai kaɗa damin a gaban Ubangiji domin yă zama yardajje a madadinku; firist ɗin zai kaɗa shi a kashegarin Asabbaci.
Canghmuei te BOEIPA mikhmuh ah thueng saeh. Nangmih taengah kolonah ham khosoih loh Sabbath vuen ah thueng saeh.
12 A ranar da kuka kaɗa damin, dole ku miƙa hadaya ta ƙonawa na ɗan rago bana ɗaya, marar lahani ga Ubangiji,
Canghmuei na thueng uh hnin vaengah tu kum khat ca te BOEIPA taengah hmueihhlutnah ham a cuemthuek la nawn uh.
13 tare da hadaya ta gari mai laushi, humushi biyu haɗe da mai, wato, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji, mai daɗin ƙanshi, da kuma abin sha kwalaba ɗaya na ruwan inabi.
Situi neh a thoek khocang vaidam doh nit te BOEIPA ham hmaihlutnah hmuehmuei botui la om saeh. Tuisi ham misurtui bunang pali khueh saeh.
14 Ba za ku ci wani burodi, ko gasasshen hatsi, ko sabon hatsi ba, sai ran nan da kuka kawo wannan hadaya ga Allahnku. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a duk inda kuke zama.
Na Pathen kah nawnnah a khohnin tuung na pha hlan atah vaidam khaw, vairhum khaw, cangthai khaw ca uh boeh. Na tolrhum boeih kah na cadilcahma ham kumhal khosing la om saeh.
15 “‘Daga kashegarin Asabbaci, ranar da kuka kawo dami don hadaya ta kaɗawa, ku ƙirga cikakku makoni bakwai.
Thueng hmueih la canghuei na khuen tue phoeikah Sabbath vuen lamkah te tae lamtah Sabbath voeirhih a cum due om sak.
16 Ku ƙirga kwana hamsin har zuwa kashegarin Asabbaci na bakwai, sa’an nan ku miƙa hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji.
Sabbath voei rhih na tae vuen kah hnin sawmnga vaengah khocang cangthai te BOEIPA taengla nawn uh.
17 Daga ko’ina kuke da zama, ku kawo dunƙule biyu na humushin gari mai laushi da aka tuya da yisti, a matsayin hadaya ta kaɗawa ta’ya’yan fari na itatuwa ga Ubangiji.
Na tolrhum lamkah thueng hmueih vaidam hluem nit, tolrhu neh a thong vaidam doh nit te BOEIPA ham thaihcuek la khuen uh.
18 Tare da wannan, ku miƙa’yan raguna bakwai, kowanne bana ɗaya-ɗaya marar lahani, bijimi da kuma raguna biyu. Za su zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, tare da hadayunsu na hatsi, da hadayunsu na sha, hadaya da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Te vaengah vaidam hluem rhih, tu kum khat aka lo ca a cuemthuek neh, saelhung khuikah vaito ca pakhat, tutal panit te khuen lamtah BOEIPA taengkah hmueihhlutnah ham om saeh. Amih kah khocang neh tuisi te khaw BOEIPA ham hmuehmuei botui hmaihlutnah la om saeh.
19 Sa’an nan ku miƙa bunsuru ɗaya na hadaya don zunubi, da’yan raguna biyu, kowanne bana ɗaya-ɗaya, don hadaya ta salama.
Te phoeiah boirhaem ham maae tal pakhat neh rhoepnah hmueih ham tu kum khat ca pumnit te nawn uh.
20 Firist zai kaɗa’yan raguna biyun a gaban Ubangiji, a matsayin hadaya ta kaɗawa, tare da burodin sababbin’ya’yan fari na itatuwan. Tsarkaken hadaya ce ga Ubangiji ga firist.
Thaihcuek buh te thueng hmueih la BOEIPA mikhmuh ah khosoih loh thueng saeh lamtah BOEIPA taengkah a cim tuca panit te tah khosoih ham la om saeh.
21 A wannan rana za ku yi taro mai tsarki, ba kuwa za ku yi aiki na kullum ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
Tekah khohnin tuung dongah a cim tingtunnah om ham hoe uh lamtah namahmih kah thohtatnah bitat boeih te tah saii uh boeh. He tah Na tolrhum boeih kah na cadilcahma ham kumhal khosing la om saeh.
22 “‘Sa’ad da kuka yi girbin gonarku, kada ku girbe har ƙarshen gefen gonar, ko ku yi kalar girbinku. Ku bar su wa matalauta da baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Na khohmuen kah cang na ah uh vaengah khaw na khohmuen te hmangrhong kaep due khap uh boeh. Cang na ah uh vaengah khaw na cang mo te boeih yoep uh boeh. Mangdaeng neh yinlai ham hnoo pauh. Kai tah nangmih kah Pathen BOEIPA ni,” a ti nah.
23 Ubangiji ya ce wa Musa,
BOEIPA loh Moses te a voek tih,
24 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar farko ga wata na bakwai, za tă zama ranar hutu, rana ce ta tuni da yin taro mai tsarki na sujada da za a fara busar ƙaho.
“Israel ca rhoek te voek lamtah thui pah. Hla hlarhih khuikah lamhmacuek hla te nangmih ham a cim tingtunnah tamlung poekkoepnah koiyaeh om saeh.
25 Kada ku yi aiki na kullum, amma ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.’”
Te vaengah thohtatnah bitat boeih tah saii uh boel lamtah BOEIPA taengah hmaihlutnah nawn ni,” a ti nah.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
Moses te BOEIPA loh a voek.
27 “Rana ta goma ta wata bakwai, za tă zama Ranar Kafara. Sai ku yi taro mai tsarki don ku yi mūsun kanku ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.
“A hla rha khuikah a hla rhih dongah khaw nangmih ham a cim tingtunnah neh dawthnah hnin te om saeh. Te vaengah na hinglu te phaep uh lamtah BOEIPA taengah hmaihlutnah nawn uh.
28 Kada ku yi aiki a ranar, gama Ranar Kafara ce, sa’ad da za a yi kafara saboda ku a gaban Ubangiji Allahnku.
Na Pathen BOEIPA kah mikhmuh ah nangmih kah te dawth ham dawthnah khohnin la a om dongah tekah khohnin tuung ah bitat pakhat khaw saii uh boeh.
29 Duk wanda bai yi mūsun kansa a wannan rana ba, dole a raba shi daga mutanensa.
Tekah khohnin tuung dongah a pum aka phaep pawt hlanghing boeih tah a pilnam lamkah khoe van saeh.
30 Zan hallaka duk wani da ya yi aiki a wannan rana daga mutanensa.
Tekah khohnin tuung dongah bitat khat khat te hlanghing khat khat loh saii mai ngawn saeh. Tedae tekah hlanghing te a pilnam khui lamkah ka milh sak ni.
31 Sam ba za ku yi wani aiki ba. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce, wa tsararraki masu zuwa, a ko’ina kuke da zama.
Bitat pakhat khaw na saii uh pawt ham te na tolrhum boeih kah na cadilcahma rhoek ham kumhal khosing la om saeh.
32 Asabbaci ne na hutu dominku, kuma dole ku yi mūsun kanku. Daga yamman rana ta tara ga wata, har zuwa yamma na biye, za ku kiyaye Asabbacinku.”
Nangmih kah koiyaeh Sabbath ah te na hinglu phaep uh. Hla ko dongkah hlaem ah tah hlaem lamloh hlaem hil na Sabbath yaeh uh,” a ti nah.
33 Ubangiji ya ce wa Musa,
BOEIPA loh Moses te a voek tih,
34 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘A ranar goma sha biyar ga wata na bakwai, za a fara Bikin Tabanakul na Ubangiji, zai kuma ɗauki kwana bakwai.
“Israel ca rhoek te voek lamtah thui pah. Hla rhih dongkah hnin hlai nga dongah pohlip khotue te BOEIPA ham hnin rhih khuiah om saeh.
35 A ranar farko za tă zama ta taro mai tsarki, kada ku yi aiki na kullum.
Khohnin lamhmacuek, a cim tingtunnah vaengah thohtatnah bitat boeih tah saii uh boeh.
36 Kwana bakwai za ku miƙa hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, a rana ta takwas, ku yi taro mai tsarki, ku kuma miƙa hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji. Wannan ranar rufewar taro ce; kada ku yi aiki na kullum.
Hnin rhih khuiah BOEIPA taengah hmaihlutnah nawn uh. Hnin rhet te nangmih kah a cim tingtunnah la om saeh. Pahong vaengah khaw BOEIPA taengah hmaihlutnah nawn uh lamtah thohtatnah bitat boeih te saii uh boeh.
37 (“‘Waɗannan su ne bukukkuwan da Ubangiji ya kafa, waɗanda za ku yi a matsayin tsarkakakkun taro, don kawo hadayun da aka yi da wuta ga Ubangiji, hadayu na ƙonawa da hadayu na hatsi, sadaka da kuma hadayu na sha, da ake bukata kowace rana.
BOEIPA kah khoning rhoek te a cim tingtunnah la hoe uh. Tekah khohnin vaengah a khohnin loh a kuek te tah hmueihhlutnah khaw, khocang hmueih neh tuisi khaw BOEIPA taengah hmaihlutnah la khuen uh.
38 Waɗannan hadayu, ƙari ne a kan waɗannan na Asabbatan Ubangiji, haɗe kuma da kyautanku, da kome da kuka yi alkawari, da kuma hadayu yardar ran da za ku ba wa Ubangiji.)
BOEIPA kah Sabbath khaw amah vaengah, nangmih kah kutdoe khaw amah vaengah, na olcaeng boeih khaw amah vaengah, na kothoh boeih khaw amah vaengah BOEIPA taengla pae uh.
39 “‘Saboda haka, farawa daga ranar goma sha biyar ga watan bakwai, bayan kun tara hatsin gona, ku yi bikin Ubangiji kwana bakwai; rana ta fari, rana hutu ce, rana ta takwas kuma rana hutu ce.
Hla rhih phoeikah hnin hlai nga dongah khohmuen kah a vuei a thaih te khoem uh bal lamtah BOEIPA kah khotue te hnin rhih lam uh. A cuek khohnin dongah koiyaeh om vetih a rhet khohnin dongah khaw koiyaeh om bal ni.
40 A rana ta fari, za ku ɗebi zaɓaɓɓun’ya’yan itatuwa daga itatuwa, da rassan dabino, rassa masu ganye, da kuma ganyayen itacen wardi na rafi, ku yi farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku, kwana bakwai.
A cuek khohnin dongah rhuepomnah thing thaih neh rhophoe bom, thing bu thing hlaeng, soklong tuirhi te namamih ham lo uh. Na Pathen BOEIPA mikhmuh ah hnin rhih khui na kohoe sakuh.
41 Za ku kiyaye bikin nan har kwana bakwai a kowace shekara ga Ubangiji. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsarraraki masu zuwa, ku kiyaye ta a wata na bakwai.
Kum khat ah hnin rhih tah BOEIPA ham khotue na lam uh ham te na cadilcahma taengah kumhal khosing la omsaeh lamtah hla rhih dongah lam uh.
42 Ku zauna a bukkoki kwana bakwai. Dukan’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa, za su zauna a bukkoki
Dungtlungim ah hnin rhih khosa uh. Israel khuikah mupoe boeih longtah dungtlungim khuiah khosa saeh.
43 don zuriyarku tă san cewa na sa Isra’ilawa suka zauna a bukkoki sa’ad da na fitar da su daga Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Te daengah ni kamah loh Egypt kho lamkah Israel ca rhoek ka mawt vaengah dungtlungim ah ka om sak te na cadilcahma loh a ming eh. Kai tah na Pathen BOEIPA ni,” a ti nah.
44 Saboda haka Musa ya sanar wa Isra’ilawa ƙayyadaddun bukukkuwan Ubangiji.
Te dongah BOEIPA kah khoning te Israel ca rhoek ham Moses loh a thui pah.