< Firistoci 22 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla aussi à Moïse, disant:
2 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
Parle à Aaron et à ses fils, afin qu’ils s’abstiennent de ce qui a été consacré par les enfants d’Israël, et qu’ils ne souillent pas le nom des choses qui me sont consacrées, qu’ils offrent eux-mêmes. Je suis le Seigneur.
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
Dis à eux et à leurs descendants: Tout homme de votre race qui s’approchera des choses qui auront été consacrées et que les enfants d’Israël auront offertes au Seigneur, mais dans lequel est une impureté, périra devant le Seigneur. C’est moi qui suis le Seigneur.
4 “‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
Un homme de la race d’Aaron qui sera lépreux ou qui aura la gonorrhée ne mangera point des choses qui m’auront été consacrées, jusqu’à ce qu’il soit guéri. Celui qui touchera un homme impur à cause d’un mort, et à qui arrivera comme il arrive dans l’usage du mariage,
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
Et qui touchera un reptile et quoi que ce soit d’impur dont le contact souille,
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
Sera impur jusqu’au soir, et ne mangera point des choses qui auront été sanctifiées; mais lorsqu’il aura lavé sa chair dans l’eau,
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
Et que le soleil sera couché, alors purifié, il mangera des choses sanctifiées, parce que c’est sa nourriture.
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
Ils ne mangeront point d’un animal crevé, et d’un animal pris par une bête sauvage, et ils ne seront point souillés par eux. C’est moi qui suis le Seigneur.
9 “‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
Qu’ils gardent mes préceptes, afin qu’ils ne soient point soumis au péché, et qu’ils ne lorsqu’ils l’auront souillé. Je suis le Seigneur qui les sanctifie.
10 “‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
Nul étranger ne mangera des choses sanctifiées, celui qui séjourne chez un prêtre et un mercenaire n’en mangeront point.
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
Mais celui que le prêtre aura acheté, et le serviteur qui sera né dans sa maison, ceux-là en mangeront.
12 In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
Si la fille d’un prêtre épouse un homme du peuple, quel qu’il soit, elle ne mangera point des choses qui auront été sanctifiées, ni des prémices.
13 Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
Mais si, veuve ou répudiée et sans enfants, elle retourne à la maison de son père, elle sera nourrie de la nourriture de son père, comme elle avait accoutumé étant jeune fille. Aucun étranger n’a le droit d’en manger.
14 “‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
Celui qui aura mangé des choses sanctifiées par ignorance, ajoutera la cinquième partie à ce qu’il a mangé, et il la donnera au prêtre pour le sanctuaire.
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
Ils ne profaneront point les choses sanctifiées des enfants d’Israël, que ceux-ci offrent au Seigneur:
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
De peur qu’ils ne portent l’iniquité de leur délit, lorsqu’ils auront mangé les choses sanctifiées. Je suis le Seigneur qui les sanctifie.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
18 “Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
Parle à Aaron, à ses fils et à tous les enfants d’Israël, et tu leur diras: Un homme de la maison d’Israël, et d’entre les étrangers qui habitent chez vous qui présente son oblation, ou acquittant des vœux, ou faisant une offrande spontanée, quoi que ce soit qu’il présente pour l’holocauste du Seigneur,
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
Afin que ce soit présenté par vous, ce sera un mâle sans tache d’entre les bœufs, les brebis et les chèvres.
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
S’il a une tache, vous ne l’offrirez point, et il ne sera point acceptable.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
Un homme qui offre une victime de sacrifices pacifiques au Seigneur, ou acquittant des vœux, ou faisant une offrande spontanée, tant de bœufs que de brebis, offrira un animal sans tache, afin qu’il soit acceptable: il n’y aura aucune tache en lui.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
S’il est aveugle, s’il a un membre rompu, ou une cicatrice, ou des pustules, ou la gale, ou le farcin: vous n’offrirez pas ces animaux au Seigneur, et vous n’en brûlerez point sur l’autel du Seigneur.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
Tu pourras offrir volontairement un bœuf et une brebis, une oreille et la queue ayant été coupées; mais un vœu ne peut être acquitté par leur moyen.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
Vous n’offrirez au Seigneur aucun animal qui a l’organe générateur ou froissé, ou foulé, ou coupé, ou arraché; et en votre pays ne faites absolument point cela.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
De la main de l’étranger vous n’offrirez point des pains à votre Dieu, ni toute autre chose qu’il voudra donner, parce que toutes ces choses sont corrompues et souillées: vous ne les recevrez point.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
Un bœuf, une brebis et une chèvre, lorsqu’ils seront nés, seront sept jours sous la mamelle de leur mère; mais au huitième jour et après, ils pourront être offerts au Seigneur.
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
Soit cette vache, soit cette brebis, elles ne seront pas immolées en un seul jour avec leurs petits.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
Si vous immolez une hostie pour action de grâces au Seigneur, afin qu’il puisse se laisser fléchir,
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
Vous la mangerez le même jour, il n’en demeurera rien pour le matin du jour suivant. Je suis le Seigneur.
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
Gardez mes commandements et exécutez-les. Je suis le Seigneur.
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
Ne souillez point mon nom saint, afin que je sois sanctifié au milieu des enfants d’Israël. Je suis le Seigneur qui vous sanctifie,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
Et qui vous ai retirés de la terre d’Egypte afin que je fusse votre Dieu. Je suis le Seigneur.

< Firistoci 22 >