< Firistoci 22 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
2 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
“Speak to Aaron and to his sons, and they are separated from the holy things of the sons of Israel, and they do not defile My holy Name in what they are hallowing to Me; I [am] YHWH.
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
Say to them: Throughout your generations, any man who draws near, out of all your seed, to the holy things which the sons of Israel sanctify to YHWH, and his uncleanness [is] on him—indeed, that person has been cut off from before My face; I [am] YHWH.
4 “‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
Any man of the seed of Aaron, and he is leprous or has discharging—he does not eat of the holy things until he is clean; and he who is coming against any uncleanness of a person, or a man whose seed [from] intercourse goes out from him,
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
or a man who comes against any teeming thing which is unclean to him, or against a man who is unclean to him, even any of his uncleanness—
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
the person who comes against it has even been unclean until the evening, and does not eat of the holy things, but has bathed his flesh with water,
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
and the sun has gone in, and he has been clean, and afterward he eats of the holy things, for it [is] his food;
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
he does not eat a carcass or torn thing, to become unclean with it; I [am] YHWH.
9 “‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
And they have kept My charge, and bear no sin for it, that they have died for it when they defile it; I [am] YHWH sanctifying them.
10 “‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
And no stranger eats of the holy thing; a settler [with] a priest and a hired worker does not eat of the holy thing;
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
but when a priest buys a person, the purchase of his money, he eats of it, also one born in his house; they eat of his bread.
12 In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
And a priest’s daughter, when she is a strange man’s, she does not eat of the raised-offering of the holy things;
13 Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
but a priest’s daughter, when she is a widow, or cast out, and has no seed, and has turned back to the house of her father, as [in] her youth, she eats of her father’s bread; but no stranger eats of it.
14 “‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
And when a man eats of a holy thing through ignorance, then he has added its fifth part to it, and has given [it] to the priest, with the holy thing;
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
and they do not defile the holy things of the sons of Israel—that which they lift up to YHWH,
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
or have caused them to bear the iniquity of the guilt-offering in their eating their holy things; for I [am] YHWH, sanctifying them.”
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
18 “Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
“Speak to Aaron, and to his sons, and to all the sons of Israel, and you have said to them: Any man of the house of Israel, or of the sojourners in Israel, who brings his offering near, of all his vows, or of all his willing offerings which they bring near to YHWH for a burnt-offering—
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
[you bring near] at your pleasure a perfect one, a male of the herd, of the sheep or of the goats;
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
nothing in which [is] blemish do you bring near, for it is not for a pleasing thing for you.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
And when a man brings a sacrifice of peace-offerings near to YHWH, to complete a special vow, or for a willing-offering, of the herd or of the flock, it is perfect for a pleasing thing: no blemish is in it.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
Blind, or broken, or maimed, or [having] an oozing sore [[or a defect of the eye]], or itch, or scab—you do not bring these near to YHWH, and you do not make a fire-offering from them on the altar to YHWH.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
As for an ox or sheep [that] is deformed or stunted—you make it a willing-offering, but it is not pleasing for a vow.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
As for bruised, or beaten, or torn, or cut—you do not bring [it] near to YHWH; and in your land you do not do it.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
And you do not bring the bread of your God near from the hand of a son of a stranger, from any of these, for their corruption [is] in them; blemish [is] in them; they are not pleasing for you.”
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
“When ox, or lamb, or goat is born, and it has been under its mother [for] seven days, then from the eighth day and from now on, it is pleasing for an offering, a fire-offering to YHWH;
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
but an ox or sheep—you do not slaughter it and its young one in one day.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
And when you sacrifice a sacrifice of thanksgiving to YHWH, you sacrifice at your pleasure;
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
it is eaten on that day—you do not leave of it until morning; I [am] YHWH.
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
And you have kept my commands and have done them; I [am] YHWH;
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
and you do not defile My holy Name, and I have been hallowed in the midst of the sons of Israel; I [am] YHWH, sanctifying you,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
who am bringing you up out of the land of Egypt, to become your God; I [am] YHWH.”

< Firistoci 22 >