< Firistoci 22 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
The Lord also spoke to Moses saying:
2 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
Speak to Aaron and to his sons, so that they may be careful of those things which have been consecrated for the sons of Israel, and so that they may not contaminate the name of the things sanctified to me, which they offer. I am the Lord.
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
Say to them and to their posterity: Every man of your stock, who approaches toward those things which have been consecrated, and which the sons of Israel have brought forward to the Lord, in whom there is uncleanness, shall perish before the Lord. I am the Lord.
4 “‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
The man of the offspring of Aaron, who is a leper or who is suffering a flow of seed, shall not eat of those things which have been sanctified to me, until he is healed. Whoever will have touched what is unclean because of the dead, and he whose seed goes out from him, as if from sexual intercourse,
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
and whoever has touched a creeping thing, or any kind of unclean thing, the touching of which is filthy,
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
shall be unclean until evening, and shall not eat those things which have been sanctified. But when he has washed his flesh with water,
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
and the sun has set, then, having been purified, he shall eat from what has been sanctified, because it is his food.
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
Whatever dies on its own, and whatever has been seized by a wild beast, they shall not eat, nor shall they be polluted by these. I am the Lord.
9 “‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
Let them observe my precepts, so that they may not fall under sin, and die in the Sanctuary, when they will have defiled it. I am the Lord, who sanctifies them.
10 “‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
No foreigner shall eat from what has been sanctified; a guest of the priests and a hired servant shall not eat from them.
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
But whomever the priest has bought, and whoever has been born into his house, these shall eat from them.
12 In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
If the daughter of a priest has been married to any of the people, she shall not eat from what has been sanctified, nor from the first-fruits.
13 Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
But if she is a widow or divorced, and, being without children, she returns to her father’s house, she shall be nourished by her father’s foods, just as she was accustomed to do as a girl. No foreigner shall have the authority to eat from them.
14 “‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
Whoever, through ignorance, eats from what has been sanctified shall add a fifth part to that which he ate, and he shall give it to the priest at the Sanctuary.
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
And they shall not contaminate what has been sanctified from the sons of Israel, which they offer to the Lord,
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
lest perhaps they may suffer the iniquity of their offense, when they will have eaten what has been sanctified. I am the Lord, who sanctifies them.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
18 “Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
Speak to Aaron, and to his sons, and to all the sons of Israel, and you shall say to them: The man from the house of Israel, or from the newcomers who live with you, who would bring forward his oblation, either fulfilling his vows or offering spontaneously, whatever he brings forward as a holocaust for the Lord,
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
in order to be offered through you, shall offer an immaculate male from the oxen, or from the sheep, or from the goats.
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
If it has a blemish, you shall not offer it, and it shall not be acceptable.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
The man who will have offered a victim of peace offerings to the Lord, either fulfilling his vows or offering spontaneously, whether of oxen, or of sheep, shall offer what is immaculate, so that it may be acceptable. There shall be no blemish in it.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
If it is blind, or if it is broken, or if it has a scar, or if it is has a boil, or a skin disease or infection, you shall not offer these to the Lord, nor shall you burn any of these upon the altar of the Lord.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
An ox or a sheep, having an amputated ear or tail, you are able to offer voluntarily, but a vow is not able to be fulfilled by these.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
You shall not offer to the Lord any animal which has the testicles bruised, or crushed, or cut and taken away, and you shall not cause any of these things in your land.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
From the hand of a foreigner, you shall not offer bread to your God, nor anything else that he would choose to give; for all this has been corrupted and blemished. You shall not accept them.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
An ox, a sheep, or a goat, when they have been born, shall be under the udder of their mother for seven days. But on the eighth day and thereafter, they are able to be offered to the Lord.
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
Whether it is an ox, or a sheep, they shall not be immolated on the same day with their newborns.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
If you immolate a victim as an act of thanksgiving to the Lord, so that he may be pleased,
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
you shall eat it on the same day; none of it shall remain until morning on the next day. I am the Lord.
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
Observe my commandments, and do them. I am the Lord.
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
Do not pollute my holy name, so that I may be sanctified in the midst of the sons of Israel. I am the Lord, who sanctifies you,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
and who led you away from the land of Egypt, so that I may be to you as God. I am the Lord.

< Firistoci 22 >