< Firistoci 22 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
2 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
Speak to Aaron and to his sons, that they separate themselves from the holy things of the sons of Israel, which they hallow to me, and that they not profane my holy name. I am Jehovah.
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
Say to them, Whoever he is of all your seed throughout your generations, that approaches to the holy things, which the sons of Israel hallow to Jehovah, having his uncleanness upon him, that soul shall be cut off from before me. I am Jehovah.
4 “‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
Whatever man of the seed of Aaron being a man with a leprous disease, or has an issue, he shall not eat of the holy things until he is clean. And whoever touches anything that is unclean by the dead, or a man whose seed goes from him,
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
or whoever touches any creeping thing, by which he may be made unclean, or a man of whom he may take uncleanness, whatever uncleanness he has,
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
the soul that touches any such shall be unclean until the evening. And shall not eat of the holy things unless he bathe his flesh in water.
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
And when the sun is down, he shall be clean, and afterward he shall eat of the holy things, because it is his bread.
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
That which dies of itself, or is torn by beasts, he shall not eat to defile himself with it. I am Jehovah.
9 “‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
They shall therefore keep my charge, lest they bear sin for it, and die in it if they profane it. I am Jehovah who sanctifies them.
10 “‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
There shall no stranger eat of the holy thing. A sojourner of the priest's, or a hired servant, shall not eat of the holy thing.
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
But if a priest buys any soul, the purchase of his money, he shall eat of it, and such as are born in his house, they shall eat of his bread.
12 In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
And if a priest's daughter be married to a stranger, she shall not eat of the heave offering of the holy things.
13 Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
But if a priest's daughter be a widow, or divorced, and have no child, and is returned to her father's house, as in her youth, she shall eat of her father's bread, but there shall no stranger eat of it.
14 “‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
And if a man eats of the holy thing unwittingly, then he shall put the fifth part of it to it, and shall give the holy thing to the priest.
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
And they shall not profane the holy things of the sons of Israel, which they offer to Jehovah,
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
and so cause them to bear the iniquity that brings guilt when they eat their holy things, for I am Jehovah who sanctifies them.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
18 “Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
Speak to Aaron, and to his sons, and to all the sons of Israel, and say to them, Whoever he is of the house of Israel, or of the sojourners in Israel, who offers his oblation, whether it be any of their vows, or any of their freewill offerings, which they offer to Jehovah for a burnt offering,
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
that ye may be accepted, ye shall offer a male without blemish, of the bullocks, of the sheep, or of the goats.
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
But whatever has a blemish, that ye shall not offer, for it shall not be acceptable for you.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
And whoever offers a sacrifice of peace offerings to Jehovah to accomplish a vow, or for a freewill offering, of the herd or of the flock, it shall be perfect to be accepted; there shall be no blemish in it.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
Blind, or broken, or maimed, or having a skin tumor, or scurvy, or scabbed, ye shall not offer these to Jehovah, nor make an offering by fire of them upon the altar to Jehovah.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
Either a bullock or a lamb that has anything superfluous or lacking in his parts, that thou may offer for a freewill offering, but it shall not be accepted for a vow.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
That which has its testicles bruised, or crushed, or broken, or cut, ye shall not offer to Jehovah, neither shall ye do thus in your land.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
Neither from the hand of a foreigner shall ye offer the bread of your God of any of these, because their corruption is in them; there is a blemish in them. They shall not be accepted for you.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
When a bullock, or a sheep, or a goat, is brought forth, then it shall be seven days under the dam, and from the eighth day and after that it shall be accepted for the oblation of an offering made by fire to Jehovah.
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
And whether it be cow or ewe, ye shall not kill it and its young both in one day.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
And when ye sacrifice a sacrifice of thanksgiving to Jehovah, ye shall sacrifice it that ye may be accepted.
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
It shall be eaten on the same day. Ye shall leave none of it until the morning. I am Jehovah.
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
Therefore ye shall keep my commandments, and do them. I am Jehovah.
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
And ye shall not profane my holy name, but I will be hallowed among the sons of Israel. I am Jehovah who hallows you,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
who brought you out of the land of Egypt, to be your God. I am Jehovah.

< Firistoci 22 >