< Firistoci 21 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
RAB Musa'ya şöyle dedi: “Harun soyundan gelen kâhinlere de ki, ‘Kâhinlerden hiçbiri yakın akrabası olan annesi, babası, oğlu, kızı ve kardeşi dışında, halkından birinin ölüsüyle kendini kirletmesin.
2 sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
Yanında kalan evlenmemiş kızkardeşi için kendini kirletebilir.
4 Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
Halkı arasında bir büyük olarak kendini kirletmemeli, adına leke getirmemeli.
5 “‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
“‘Kâhinler yas tutarken başlarını tıraş etmeyecek, sakallarının uçlarını kesmeyecek, bedenlerini yaralamayacaklar.
6 Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
Tanrıları için kutsal olacaklar, Tanrıları'nın adını lekelemeyecekler. Çünkü onlar Tanrıları RAB'be yakılan sunu ve yiyecek sunusu sunuyorlar. Kutsal olmaları gerekir.
7 “‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
Kâhinler fahişelerle, kirletilmiş kadınlarla, boşanmış kadınlarla evlenmeyecek. Çünkü kâhin Tanrı için kutsal olmalıdır.
8 An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
Onu kutsal sayın. Çünkü yiyecek sunusunu Tanrınız'a o sunuyor. Sizin için kutsaldır. Çünkü ben kutsalım, sizi kutsal kılan RAB benim.
9 “‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
Bir kâhinin kızı fahişelik yaparak kendini kirletirse, hem kendini hem de babasını rezil etmiş olur. Yakılmalıdır.
10 “‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
“‘Öbür kâhinler arasından başına mesh yağı dökülen ve özel giysiler giymek üzere atanan başkâhin, saçlarını dağıtmayacak, giysilerini yırtmayacak.
11 Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
Hiçbir ölüye yaklaşmayacak. Ölen annesi, babası bile olsa kendini kirletmeyecek.
12 An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
Tapınak hizmetinden ayrılmayacak, Tanrısı'nın Tapınağı'nı kirletmeyecek. Çünkü Tanrı'nın buyurduğu mesh yağıyla Tanrısı'na adanmıştır. RAB benim.
13 “‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
Başkâhinin evleneceği kadın bakire olmalıdır.
14 Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
Dul, boşanmış, kirletilmiş ya da fahişe bir kadınla evlenmeyecek. Yalnız kendi halkından bakire bir kızla evlenebilir.
15 don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
Böylece halkının arasında çocuklarına leke sürmemiş olur. Onu kutsal kılan RAB benim.’”
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
RAB Musa'ya şöyle dedi:
17 “Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
“Harun'a de ki, ‘Soyundan gelecek kuşaklar boyunca kusurlu olan hiç kimse yiyecek sunusu sunmak üzere Tanrısı'na yaklaşmasın.
18 Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
Kusurlu olan, sunağa yaklaşamaz: Kör, topal, yüzü arızalı, organlarından biri aşırı büyümüş,
19 ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
kolu veya ayağı kırık,
20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
kambur, cüce, gözü özürlü, uyuz, yarası kabuk bağlamış ya da hadım.
21 Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
Kâhin Harun'un soyundan bu kusurlara sahip hiç kimse RAB için yakılan sunuyu sunmak üzere sunağa yaklaşmayacak. Çünkü kusurludur. Tanrısı'na yiyecek sunusu sunmak üzere sunağa yaklaşamaz.
22 Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
Böyle bir adam Tanrısı'na sunulan kutsal ve en kutsal yiyecekleri yiyebilir.
23 duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
Ancak perdeye ve sunağa yaklaşmayacaktır. Çünkü kusurludur. Tapınağımı kirletmesin. Onları kutsal kılan RAB benim.’”
24 Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.
Musa Harun'la oğullarına ve bütün İsrail halkına bunları anlattı.

< Firistoci 21 >