< Firistoci 21 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
INkosi yasisithi kuMozisi: Tshono kubapristi, amadodana kaAroni, uthi kubo: Kakungabi khona ozingcolisayo ngofileyo phakathi kwabantu bakibo,
2 sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
ngaphandle kwesihlobo sakhe, esiseduze laye, ngonina, langoyise, langendodana yakhe, langendodakazi yakhe, langomfowabo,
3 ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
langodadewabo intombi emsulwa, eseduze laye, engazange ibe ngeyendoda; angazingcolisa ngayo.
4 Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
Kayikuzingcolisa, eyisikhulu phakathi kwabantu bakibo, ukuzingcolisa.
5 “‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
Kabayikwenza impabanga ekhanda labo, bangageli igumbi lodevu lwabo, bangacabi inhlanga enyameni yabo.
6 Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
Bazakuba ngcwele kuNkulunkulu wabo, bangeyisi ibizo likaNkulunkulu wabo. Ngoba banikela iminikelo yeNkosi eyenziwe ngomlilo, ukudla kukaNkulunkulu wabo. Ngakho bazakuba ngcwele.
7 “‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
Kabayikuthatha owesifazana oyisifebe kumbe ongcolileyo, njalo kabayikuthatha owesifazana olahlwe yindoda yakhe; ngoba ungcwele kuNkulunkulu wakhe.
8 An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
Ngakho uzamngcwelisa, ngoba unikela ukudla kukaNkulunkulu wakho. Uzakuba ngcwele kuwe, ngoba mina Nkosi elingcwelisayo ngingcwele.
9 “‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
Lendodakazi yaloba nguwuphi umpristi, uba izingcolisa ngokuphinga, iyamngcolisa uyise; izatshiswa ngomlilo.
10 “‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
Lompristi omkhulu phakathi kwabafowabo, okuthelwe ekhanda lakhe amafutha okugcoba, lowehlukaniselwa ukuthi embathe izembatho, kayikuvumela ukuthi ikhanda lakhe lembulwe, angadabuli izembatho zakhe;
11 Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
angayi lakusiphi isidumbu, angazingcolisi ngoyise loba ngonina;
12 An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
angaphumi endlini engcwele, angangcolisi indlu engcwele kaNkulunkulu wakhe, ngoba umqhele wamafutha okugcoba kaNkulunkulu wakhe uphezu kwakhe. NgiyiNkosi.
13 “‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
Njalo yena uzathatha umfazi ebuntombini bakhe.
14 Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
Umfelokazi, kumbe olahliweyo, loba isifebe esingcolisiweyo, laba kangabathathi. Kodwa uzathatha intombi emsulwa ebantwini bakibo ibe ngumkakhe,
15 don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
njalo angangcolisi inzalo yakhe phakathi kwabantu bakibo. Ngoba ngiyiNkosi emngcwelisayo.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
17 “Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
Khuluma kuAroni usithi: Loba ngubani owenzalo yakho ezizukulwaneni zabo okulesici kuye kangasondeli ukunikela ukudla kukaNkulunkulu wakhe.
18 Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
Ngoba loba nguwuphi umuntu okulesici kuye angasondeli, umuntu oyisiphofu, kumbe oyisiqhuli, kumbe olimele ebusweni, kumbe olesitho eselulekileyo,
19 ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
kumbe umuntu okulokwephuka konyawo kuye, kumbe ukwephuka kwesandla,
20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
kumbe olesifumbu, kumbe ongumuthwa, kumbe olomntwana elihlweni lakhe, kumbe olentembuzane, kumbe oloqweqwe olulumayo, loba olimele emasendeni.
21 Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
Kakulamuntu owenzalo kaAroni umpristi okukuye isici ozasondela ukunikela iminikelo yeNkosi eyenziwe ngomlilo; kulesici kuye, angasondeli ukunikela ukudla kukaNkulunkulu wakhe.
22 Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
Angadla ukudla kukaNkulunkulu wakhe, ezintweni ezingcwelengcwele lezintweni ezingcwele,
23 duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
kodwa angezi kulo iveyili, angasondeli elathini, ngoba kulesici kuye, ukuze angangcolisi izindlu zami ezingcwele. Ngoba ngiyiNkosi ebangcwelisayo.
24 Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.
UMozisi wasekhuluma lokho kuAroni, lakumadodana akhe, lakubo bonke abantwana bakoIsrayeli.

< Firistoci 21 >