< Firistoci 21 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
Yahweh dit à Moïse: « Parle aux prêtres, fils d’Aaron, et dis-leur: Nul ne se rendra impur au milieu de son peuple pour un mort,
2 sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
excepté pour son parent du même rang, pour sa mère, pour son père, pour son fils, pour sa fille, pour son frère,
3 ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
et pour sa sœur vierge, qui vit auprès de lui, n’étant pas encore mariée; pour elle il se rendra impur.
4 Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
Chef de maison parmi son peuple, il ne se souillera pas et ne profanera pas sa dignité.
5 “‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
Les prêtres ne se raseront pas la tête, ils n’enlèveront pas les côtés de leur barbe, et ils ne feront pas d’incisions dans leur chair.
6 Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
Ils seront saints pour leur Dieu, et ils ne profaneront pas le nom de leur Dieu, car ils offrent à Yahweh des sacrifices consumés par le feu, le pain de leur Dieu: ils seront saints.
7 “‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
Ils ne prendront point une femme prostituée ou déshonorée; ils ne prendront point une femme répudiée par son mari, car le prêtre est saint pour son Dieu.
8 An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
Tu le tiendras pour saint, car il offre le pain de ton Dieu; il sera saint pour toi, car je suis saint, moi Yahweh, qui vous sanctifie.
9 “‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
Si la fille d’un prêtre se déshonore en se prostituant, elle déshonore son père: elle sera brûlée au feu.
10 “‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
Le grand prêtre qui est au-dessus de ses frères, sur la tête duquel a été répandue l’huile d’onction, et qui a été installé pour revêtir les vêtements sacrés, ne découvrira pas sa tête et ne déchirera pas ses vêtements.
11 Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
Il n’approchera d’aucun mort; il ne se rendra impur ni pour son père, ni pour sa mère.
12 An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
Il ne sortira pas du sanctuaire, et ne profanera pas le sanctuaire de son Dieu, car l’huile d’onction de son Dieu est un diadème sur lui. Je suis Yahweh.
13 “‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
Il prendra pour femme une vierge.
14 Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
Il ne prendra ni une veuve, ni une femme répudiée, ni une femme déshonorée ou prostituée; mais il prendra pour femme une vierge du milieu de son peuple.
15 don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
Il ne déshonorera pas sa postérité au milieu de son peuple; car je suis Yahweh, qui le sanctifie. »
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh parla à Moïse, en disant:
17 “Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
« Parle à Aaron, et dis- lui: Nul homme de ta race, dans toutes les générations, qui aura une difformité corporelle, n’approchera pour offrir le pain de ton Dieu.
18 Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
Car nul homme qui a une difformité corporelle n’approchera: un homme aveugle ou boiteux, ou qui aura une mutilation ou une excroissance;
19 ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
ou un homme qui aura une fracture au pied ou à la main;
20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
qui sera bossu ou nain, ou qui aura une tache à l’œil, la gale, une dartre ou les testicules écrasés.
21 Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
Nul homme de la race du prêtre Aaron qui aura une difformité corporelle, ne s’approchera pour offrir à Yahweh les sacrifices faits par le feu; il a une difformité corporelle: qu’il ne s’approche point pour offrir le pain de son Dieu.
22 Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
Il pourra manger le pain de son Dieu, des choses très saintes et des choses saintes.
23 duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
Mais il n’ira point vers le voile et ne s’approchera point de l’autel, car il a une difformité corporelle; il ne profanera point mes sanctuaires, car je suis Yahweh; qui les sanctifie. »
24 Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.
Ainsi parla Moïse à Aaron et à ses fils, et à tous les enfants d’Israël.

< Firistoci 21 >