< Firistoci 21 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
And Jehovah said to Moses, Speak to the priests, the sons of Aaron, and say to them, There shall none defile himself for the dead among his people,
2 sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
except for his kin, who is near to him: for his mother, and for his father, and for his son, and for his daughter, and for his brother.
3 ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
And for his sister a virgin, who is near to him, who has had no husband, for her he may defile himself.
4 Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
He shall not defile himself, who is a chief man among his people, to profane himself.
5 “‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
They shall not make baldness upon their head, neither shall they shave off the corner of their beard, nor make any cuttings in their flesh.
6 Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
They shall be holy to their God, and not profane the name of their God. For they offer the offerings of Jehovah made by fire, the bread of their God. Therefore they shall be holy.
7 “‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
They shall not take a woman who is a harlot, or profane, neither shall they take a woman put away from her husband, for he is holy to his God.
8 An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
Thou shall sanctify him therefore, for he offers the bread of thy God. He shall be holy to thee, for I Jehovah, who sanctify you, am holy.
9 “‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
And the daughter of any priest, if she profanes herself by playing the harlot, she profanes her father. She shall be burnt with fire.
10 “‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
And he who is the high priest among his brothers, upon whose head the anointing oil is poured, and who is consecrated to put on the garments, shall not let the hair of his head go loose, nor tear his clothes,
11 Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
neither shall he go in to any dead body, nor defile himself for his father, or for his mother,
12 An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
neither shall he go out of the sanctuary, nor profane the sanctuary of his God, for the crown of the anointing oil of his God is upon him. I am Jehovah.
13 “‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
And he shall take a wife in her virginity.
14 Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
A widow, or one divorced, or a profane woman, a harlot, these he shall not take, but he shall take to wife a virgin of his own people.
15 don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
And he shall not profane his seed among his people, for I am Jehovah who sanctifies him.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Jehovah spoke to Moses, saying,
17 “Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
Speak to Aaron, saying, Whoever he is of thy seed throughout their generations who has a blemish, let him not approach to offer the bread of his God.
18 Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
For whatever man he is who has a blemish, he shall not approach: not a blind man, or a lame man, or he who has a flat nose, or anything superfluous,
19 ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
or a man who is broken-footed, or broken-handed,
20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
or crook-backed, or a dwarf, or who has a blemish in his eye, or is scurvy, or scabbed, or has his testicles broken.
21 Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
No man of the seed of Aaron the priest, who has a blemish, shall come near to offer the offerings of Jehovah made by fire; he has a blemish, he shall not come near to offer the bread of his God.
22 Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
He shall eat the bread of his God, both of the most holy, and of the holy,
23 duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
only he shall not go in to the veil, nor come near to the altar, because he has a blemish, that he not profane my sanctuaries, for I am Jehovah who sanctifies them.
24 Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.
So Moses spoke to Aaron, and to his sons, and to all the sons of Israel.

< Firistoci 21 >