< Firistoci 20 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Og Herren talte til Moses og sa:
2 “Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikin Isra’ila da ya miƙa wani daga cikin’ya’yansa wa Molek, dole sa kashe shi. Mutanen ƙasar za su jajjefe shi.
Du skal si til Israels barn: Om nogen av Israels barn eller av de fremmede som bor i Israel, gir noget av sine barn fra sig til Molok, skal han late livet; folket i landet skal stene ham.
3 Zan yi gāba da wannan mutum, zan kuma raba shi da mutanensa; gama ta wurin miƙa’ya’yansa ga Molek, ya ƙazantar da wuri mai tsarkina, ya kuma ƙazantar da sunana mai tsarki.
Jeg vil sette mitt åsyn mot den mann og utrydde ham av hans folk fordi han har gitt sitt barn fra sig til Molok og gjort min helligdom uren og vanhelliget mitt hellige navn.
4 In mutanen ƙasar suka kau da idanunsu sa’ad da wannan mutum ya miƙa’ya’yansa ga Molek, suka kāsa kashe shi,
Om folket i landet lukker øinene til og ikke straffer en sådan mann med døden når han gir sitt barn fra sig til Molok,
5 zan yi gāba da wannan mutum da iyalinsa, zan raba shi da kuma duk waɗanda suka bi shi cikin karuwanci ga Molek daga mutanensu.
da vil jeg sette mitt åsyn mot denne mann og hans slekt, og ham og alle dem som følger ham i å drive avgudsdyrkelse med Molok, vil jeg utrydde av deres folk.
6 “‘Zan yi gāba da mutumin da ya juyo ga masu duba da bokaye, don yă yi karuwanci ta wurin bin su, zan kuma raba shi daga mutanensa.
Når nogen vender sig til dødningemanere og sannsigere og driver avgudsdyrkelse med dem, da vil jeg sette mitt åsyn mot den mann og utrydde ham av hans folk.
7 “‘Ku tsarkake kanku, ku kuma zama da tsarki, gama Ni ne Ubangiji Allahnku.
I skal hellige eder og være hellige; for jeg er Herren eders Gud.
8 Ku kiyaye farillaina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
Og I skal ta vare på mine lover og holde dem; jeg er Herren, som helliger eder.
9 “‘In wani ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi. Domin ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, alhakin jininsa zai zauna a kansa.
Hver den som banner sin far eller sin mor, skal late livet; sin far og sin mor har han bannet, hans blod være over ham!
10 “‘In mutum ya yi zina da matar wani, da matar maƙwabcinsa, dole a kashe su biyu da suka yi zinan.
Når en mann driver hor med en annen manns hustru - med sin næstes hustru, da skal de begge late livet, både mannen og kvinnen som har drevet hor.
11 “‘In mutum ya kwana da matar mahaifinsa, ya ƙasƙantar da mahaifinsa. Dole a kashe shi da macen, alhakin jininsu zai zauna a kansu.
Når en mann ligger hos sin fars hustru, har han vanæret sin fars leie; de skal begge late livet, deres blod være over dem!
12 “‘In mutum ya kwana da matar ɗansa, dole a kashe su biyun. Abin da suka yi haram ne; alhakin jininsu zai zauna a kansu.
Når en mann ligger hos sin sønnekone, skal de begge late livet; de har gjort en vederstyggelig gjerning, deres blod være over dem!
13 “‘In mutum ya kwana da mutum kamar yadda ake kwana da mace, su biyun sun yi abin ƙyama. Dole a kashe su, alhakin jininsu zai zauna a kansu.
Når en mann ligger hos en annen mann som en ligger hos en kvinne, da har de begge gjort en vederstyggelig gjerning; de skal late livet, deres blod være over dem!
14 “‘In mutum ya auri’ya da mahaifiyarta, mugun abu ne. Da shi da su, dole a ƙone su da wuta, saboda kada mugun abu yă kasance a cikinku.
Når en mann tar både mor og datter til ekte, da er det skammelig ferd; både han og kvinnene skal brennes med ild; slik skam skal ikke finnes blandt eder.
15 “‘In mutum ya yi jima’i da dabba, dole a kashe shi, dole kuma ku kashe dabbar.
En mann som har omgang med et dyr, skal late livet, og dyret skal I drepe.
16 “‘In mace ta kusaci dabba don tă yi jima’i da ita, ku kashe macen da dabbar. Dole a kashe su; alhakin jininsu zai zauna a kansu.
Når en kvinne kommer nær noget dyr og har omgang med det, da skal du slå ihjel både kvinnen og dyret; de skal late livet, deres blod være over dem!
17 “‘In mutum ya auri’yar’uwarsa, ko’yar mahaifinsa, ko kuwa ta mahaifiyarsa, suka kuma yi jima’i, abin kunya ne. Dole a raba su a idanun mutanensu. Ya ƙasƙantar da’yar’uwarsa kuma za a nemi hakki daga gare shi.
Når en mann tar sin søster, sin fars eller sin mors datter, til ekte og har omgang med henne, og hun med ham, da er det skammelig ferd, og de skal utryddes for sitt folks øine; han har hatt omgang med sin søster, han skal lide for sin misgjerning.
18 “‘In mutum ya kwana da mace a lokacin al’adarta, duka biyunsu za a kore su daga cikin jama’arsu, gama sun karya ƙa’idodi a kan rashi tsarki.
Når en mann ligger hos en kvinne som har sin månedlige urenhet, og har omgang med henne, da har han avdekket hennes kilde, og hun har avdekket sitt blods kilde; de skal begge utryddes av sitt folk.
19 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, ko ta mahaifinka, gama wannan zai ƙasƙantar da dangi na kurkusa, dukanku za ku ɗauki laifin.
Din mors eller din fars søster skal du ikke ha omgang med, for den som gjør dette, vanærer sin nærmeste slekt; de skal lide for sin misgjerning.
20 “‘In mutum ya kwana da bābarsa, ya ƙasƙantar da kawunsa ke nan. Hakkin zai kasance a kansu, za su mutu babu’ya’ya.
Når en mann ligger hos sin farbrors hustru, har han vanæret sin farbror; de skal lide for sin synd, de skal dø barnløse.
21 “‘In mutum ya auri matar ɗan’uwansa, aikin rashin tsabta ne, ya ƙasƙantar da ɗan’uwansa ke nan. Za su mutu babu’ya’ya.
Når en mann tar sin brors hustru, da er det skamløs ferd; han har vanæret sin bror, de skal være barnløse.
22 “‘Ku kiyaye dukan farillaina da dokokina duka, don kada ƙasar da nake kai ku ta amayar da ku.
I skal ta vare på alle mine lover og alle mine bud og holde dem, forat ikke landet skal utspy eder, det land som jeg fører eder til og vil la eder bo i,
23 Kada ku yi zama bisa ga al’adun al’umman da zan kora a gabanku. Domin sun aikata dukan waɗannan abubuwa, na yi ƙyamarsu.
og I skal ikke følge det folks skikker som jeg driver ut for eder; for alt dette har de gjort, og jeg vemmedes ved dem,
24 Amma na faɗa muku, “Za ku mallaki ƙasarsu, zan ba ku ita gādo, ƙasa mai zub da madara da zuma.” Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya keɓe ku daga al’ummai.
og jeg sa til eder: I skal ta deres land i eie, og jeg vil gi eder det til eiendom, et land som flyter med melk og honning; jeg er Herren eders Gud, som har skilt eder ut fra folkene.
25 “‘Saboda haka sai ku bambanta tsakanin dabbobi masu tsarki da marasa tsarki, da kuma tsakanin tsuntsaye masu tsarki da marasa tsarki. Kada ku ƙazantar da kanku ta wurin wata dabba, ko tsuntsu, ko wani abin da yake rarrafe a ƙasa, waɗanda na keɓe a matsayi marasa tsarki a gare ku.
Derfor skal I skille mellem rene dyr og urene og mellem urene fugler og rene og ikke gjøre eder selv vederstyggelige ved å ete de firføtte dyr eller de fugler eller det kryp på jorden som jeg har skilt ut for eder, forat I skal holde dem for urene.
26 Ku zama tsarkakakke gare ni, gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, na kuma keɓe ku daga al’ummai don ku zama nawa.
I skal være hellige for mig; for jeg, Herren, er hellig, og jeg har skilt eder ut fra folkene, forat I skal høre mig til.
27 “‘Namiji, ko ta macen da yake mai duba, ko maita a cikinku dole a kashe. Za ku jajjefe su da duwatsu; alhakin jininsu zai zauna a kansu.’”
Når det i en mann eller kvinne er en dødningemaner-ånd eller en sannsiger-ånd, da skal de late livet; de skal stenes, deres blod være over dem!

< Firistoci 20 >