< Firistoci 19 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
The Lord spak to Moises, and seide,
2 “Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
Speke thou to al the cumpenye of the sones of Israel, and thou schalt seie to hem, Be ye hooli, for Y am hooli, youre Lord God.
3 “‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Ech man drede his fadir and his modir. Kepe ye my sabatis; Y am youre Lord God.
4 “‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Nyle ye be turned to ydols, nether ye schulen make to you yotun goddis; Y am youre Lord God.
5 “‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
If ye offren a sacrifice of pesible thingis to the Lord, that it be quemeful,
6 Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
ye schulen ete it in that day, in which it is offrid, and in the tother dai; sotheli what euer thing is residue in to the thridde dai, ye schulen brenne in fier.
7 In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
If ony man etith therof aftir twei daes, he schal be vnhooli, and gilti of vnfeithfulnes `ether wickidnesse; and he schal bere his wickidnesse,
8 Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
for he defoulide the hooli thing of the Lord, and his soule schal perische fro his puple.
9 “‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
Whanne thou schalt repe the fruytis of thi lond, thou schalt not kitte `til to the ground the corn of the lond, nether thou schalt gadere the eeris of corn that ben left;
10 Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
nethir in thi vyner thou schalt gadere reysyns and greynes fallynge doun, but thou schalt leeue to be gaderid of pore men and pilgryms; Y am youre Lord God.
11 “‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
Ye schulen not do thefte. Ye schulen not lye, and no man disseyue his neiybour.
12 “‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Thou schalt not forswere in my name, nethir thou schalt defoule the name of thi God; Y am the Lord.
13 “‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
Thou schalt not make fals chalenge to thi neiybore, nethir thou schalt oppresse hym bi violence. The werk of thin hirid man schal not dwelle at thee til the morewtid.
14 “‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Thou schalt not curse a deef man, nether thou schalt sette an hurtyng bifor a blynd man; but thou schalt drede thi Lord God, for Y am the Lord.
15 “‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
Thou schalt not do that, that is wickid, nether thou schalt deme vniustli; biholde thou not the persoone of a pore man, nethir onoure thou the face of a myyti man; deme thou iustli to thi neiybore.
16 “‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
Thou schalt not be a sclaunderere, nether a priuey bacbitere in the puplis; thou schalt not stonde ayens the blood of thi neiybore; Y am the Lord.
17 “‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
Thou schalt not hate thi brothir in thin herte, but repreue hym opynly, lest thou haue synne on hym.
18 “‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
Thou schalt not seke veniaunce, nether thou schalt be myndeful of the wrong of thi cyteseyns; thou schalt loue thi freend as thi silf; Y am the Lord.
19 “‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
Kepe ye my lawis. Thou schalt not make thi beestis to gendre with the lyuynge beestis of another kynde. Thou schalt not sowe the feeld with dyuerse sede. Thou schalt not be clothid in a cloth, which is wouun of twei thingis.
20 “‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
If a man slepith with a womman by fleischly knowyng of seed, which womman is an `hand maide, ye, a noble womman of kyn, and netheles is not ayenbouyt bi prijs, nethir rewardid with fredom, bothe schulen be betun, and thei schulen not die, for sche was not fre.
21 Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
Sotheli the man for his trespas schal offre a ram to the Lord, at the dore of the tabernacle of witnessyng;
22 Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
and the preest schal preye for hym, and for his trespas, bifor the Lord; and the Lord schal be merciful to hym, and the synne schal be foryouun.
23 “‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
Whanne ye han entrid in to the lond of biheest, and han plauntid therynne appil trees, ye schulen do awei the firste flouris; the applis whiche tho trees bryngen forth, schulen be vncleene to you, nethir ye schulen ete of tho.
24 A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
Forsothe in the fourthe yeer al the fruyt of tho trees schal be `halewid preiseful to the Lord;
25 Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
forsothe in the fifthe yeer ye schulen ete fruytis, and schulen gadere applis, whiche tho trees bryngen forth; Y am youre Lord God.
26 “‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
Ye schulen not ete fleisch with blood. Ye schulen not make veyn diuynyng, nether ye schulen kepe dremes;
27 “‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
nether ye schulen clippe the heer in round, nether ye schulen schaue the beerd;
28 “‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
and on deed men ye schulen not kitte youre fleischis, nether ye schulen make to you ony fyguris, ether markis in youre fleisch; Y am the Lord.
29 “‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
Sette thou not thi douytir to do leccherie for hire, and the lond be defoulid, and be fillid with synne.
30 “‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
Kepe ye my sabatis, and drede ye my seyntuarie; Y `am the Lord.
31 “‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Bowe ye not to astronomyers, nether axe ye ony thing of fals dyuynours, that ye be defoulid bi hem; Y am youre Lord God.
32 “‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Rise thou bifor an hoor heed, and onoure thou the persoone of an eld man, and drede thou thi Lord God; Y am the Lord.
33 “‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
If a comelyng enhabitith in youre lond, and dwellith among you, dispise ye not hym,
34 Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
but be he among you as a man borun in the lond; and ye schulen loue hym as you silf, for also ye weren comelyngis in the lond of Egipt; Y am youre Lord God.
35 “‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
Nyle ye do ony wickid thing in doom, in reule, in weiyte, and in mesure; the balance be iust,
36 Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
and the weiytis be euene, the buschel be iust, and the sextarie be euene; Y am youre Lord God, that ladde you out of the lond of Egipt.
37 “‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”
Kepe ye alle myn heestis, and alle domes, and do ye tho; Y am the Lord.