< Firistoci 19 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And Yahweh spake unto Moses, saying:
2 “Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
Speak unto all the assembly of the sons of Israel and thou shalt say unto them—Holy, shall ye be, —For holy, am I—Yahweh—your God
3 “‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Ye shall, every one, revere, his father and his mother, And my sabbaths, shall ye observe, —I—Yahweh, am your God.
4 “‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Do not turn unto things of nought, And, molten gods, shall ye not make to yourselves, —I—Yahweh, am your God.
5 “‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
And when ye would offer a peace-offering unto Yahweh, ye shall offer it that ye may be accepted.
6 Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
On the day, ye offer it, shall it be eaten, and on the morrow, —but, that which remaineth until the third day, in fire, shall be consumed.
7 In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
And, if it, be eaten, on the third day, unclean, it is it shall not be accepted,
8 Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
But he that eateth it, his iniquity, shall bear, because that which had been hallowed unto Yahweh, hath he profaned, —so then that person shall be cut off from among his kinsfolk.
9 “‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
And when ye reap the harvest of your land, thou shalt not wholly clear the border of thy field, in reaping, —nor shalt thou gather up the gleaning of thy harvest.
10 Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
And, thy vineyard, shalt thou not go over again, nor gather, every single grape: for the poor and for the sojourner, shalt thou leave them, I—Yahweh, am your God.
11 “‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
Ye shall not steal, —nor deceive nor lie one man to another;
12 “‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Nor swear by my name falsely, —And so profane the name of thy God: I, am Yahweh.
13 “‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
Thou shalt not oppress thy neighbour nor rob [him], —The wages of him that is hired shall not tarry with thee, until the morning.
14 “‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not curse the deaf, Nor, before the blind, place a stumbling-block, —So shalt thou stand in awe of thy God I, am Yahweh.
15 “‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
Ye shall not act perversely in giving judgment, Thou shalt neither respect the person of the poor, Nor prefer the person of the great, —In righteousness, shalt thou judge thy neighbour.
16 “‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not go about talebearing, among thy people Thou shalt not stand by, over the blood of thy neighbour: I, am Yahweh.
17 “‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
Thou shalt not hate thy brother in thy heart, —Thou shalt, faithfully reprove, thy neighbour, and not countenance him in sin:
18 “‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not take vengeance neither shalt thou cherish anger against the sons of thy people, So shalt thou love thy neighbour as thyself, —I, am Yahweh.
19 “‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
My statutes, shall ye observe, Thy beasts, shalt thou not cause to breed in two kinds, Thy field, shalt thou not sow with two sorts of seed, —And a garment woven of diverse threads, shalt thou not suffer to come upon thee.
20 “‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
And whosoever lieth carnally with a woman, she being a bondmaid, acquired for a husband, and neither, redeemed, nor, freedom, given her, inquisition, shall be made they shall not be put to death, because she was not free;
21 Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
but he shall bring in his guilt-bearer unto Yahweh, unto the entrance of the tent of meeting, —even a ram as a guilt-bearer;
22 Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
and the priest shall put a propitiatory-covering over him with the guilt-bearing ram before Yahweh, on account of his sin which he hath committed, —so shall he have forgiveness, from his sin which he hath committed.
23 “‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
And when ye come into the land, and plant any manner of fruit-tree, then shall ye count as uncircumcised the fruit thereof, three years, shall it be to you as if unclean, it shall not be eaten.
24 A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
But, in the fourth year, all the fruit thereof shall be hallowed for a festival of thanksgiving unto Yahweh.
25 Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
And in the fifth year, shall ye eat the fruit thereof, that it may enrich you with its increase, —I—Yahweh, am your God.
26 “‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
Ye shall eat nothing with the blood thereof, —Ye shall not practise divination neither shall ye use magic.
27 “‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
Ye shall not shave in a circle around your head, —nor shalt thou disfigure the fringe of thy beard.
28 “‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
Cuttings for a dead person, shall ye not make in your flesh. And punctures in your persons, shall ye not print, —I, am Yahweh.
29 “‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
Do not profane thy daughter by causing her to be unchaste, —lest the land fall to unchastity, and so the land be filled with wickedness.
30 “‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
My sabbaths, shall ye observe, And my sanctuary, shall ye revere, —I, am Yahweh.
31 “‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Do not turn unto mediums, Nor, for oracles, make search, To render yourselves unclean with them, I—Yahweh, am your God.
32 “‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Before a hoary head, shalt thou rise up, And shalt honour the presence of an elder, —So shalt thou stand in awe of thy God—I, am Yahweh.
33 “‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
And, when there sojourneth with thee a sojourner in your land, ye shall not oppress him:
34 Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
As one home born from among yourselves, shall be unto you the sojourner who sojourneth with you, So shalt thou love him as thyself, For, sojourners, became ye, in the land of Egypt, —I—Yahweh, am your God.
35 “‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
Ye shall not act perversely in giving judgment, —in measures of extent, in weights in measures of capacity:
36 Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
Just balances, just weights, a just ephah and a just hin, shall ye have, —I—Yahweh, am your God, who brought you forth out of the land of Egypt.
37 “‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”
Therefore shall ye observe all my statutes and all my regulations and do them, —I, am Yahweh.