< Firistoci 19 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
The Lord spoke to Moses, saying:
2 “Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
Speak to all the congregation of the children of Israel, and thou shalt say to them: Be ye holy, because I the Lord your God am holy.
3 “‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Let every one fear his father, and his mother. Keep my sabbaths. I am the Lord your God.
4 “‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Turn ye not to idols, nor make to yourselves molten gods. I am the Lord your God.
5 “‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
If ye offer in sacrifice a peace offering to the Lord, that he may be favourable,
6 Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
You shall eat it on the same day it was offered, and the next day: and whatsoever shall be left until the third day, you shall burn with fire.
7 In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
If after two days ally man eat thereof, he shall be profane and guilty of impiety:
8 Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
And shall bear his iniquity, because he hath defiled the holy thing of the Lord, and that soul shall perish from among his people.
9 “‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
When thou reapest the corn of thy land, thou shalt not cut down all that is on the face of the earth to the very ground: nor shalt thou gather the ears that remain.
10 Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Neither shalt thou gather the bunches and grapes that fall down in thy vineyard, but shalt leave them to the poor and the strangers to take. I am the Lord your God.
11 “‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
You shall not steal. You shall not lie, neither shall any man deceive his neighbour.
12 “‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not swear falsely by my name, nor profane the name of thy God. I am the Lord.
13 “‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
Thou shalt not calumniate thy neighbour, nor oppress him by violence. The wages of him that hath been hired by thee shall not abide with thee until the morning.
14 “‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not speak evil of the deaf, nor put a stumblingblock before the blind: but thou shalt fear the Lord thy God, because I am the Lord.
15 “‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
Thou shalt not do that which is unjust, nor judge unjustly. Respect not the person of the poor, nor honour the countenance of the mighty. But judge thy neighbour according to justice.
16 “‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
Thou shalt not be a detractor nor a whisperer among the people. Thou shalt not stand against the blood of thy neighbour. I am the Lord.
17 “‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
Thou shalt not hate thy brother in thy heart, but reprove him openly, lest thou incur sin through him.
18 “‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
Seek not revenge, nor be mindful of the injury of thy citizens. Thou shalt love thy friend as thyself. I am the Lord.
19 “‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
Keep ye my laws. Thou shalt not make thy cattle to gender with beasts of any other kind. Thou shalt not sow thy field with different seeds. Thou shalt not wear a garment that is woven of two sorts.
20 “‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
If a man carnally lie with a woman that is a bondservant and marriageable, and yet not redeemed with a price, nor made free: they both shall be scourged, and they shall not be put to death, because she was not a free woman.
21 Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
And for his trespass he shall offer a ram to the Lord, at the door of the tabernacle of the testimony:
22 Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
And the priest shall pray for him and for his sin before the Lord, and he shall have mercy on him, and the sin shall be forgiven.
23 “‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
When you shall be come into the land, and shall have planted in it fruit trees, you shall take away the firstfruits of them: the fruit that comes forth shall be unclean to you, neither shall you eat of them.
24 A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
But in the fourth year, all their fruit shall be sanctified, to the praise of the Lord.
25 Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
And in the fifth year you shall eat the fruits thereof, gathering the increase thereof. I am the Lord your God.
26 “‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
You shall not eat with blood. You shall not divine nor observe dreams.
27 “‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
Nor shall you cut your hair roundwise: nor shave your beard.
28 “‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
You shall not make any cuttings in your flesh, for the dead, neither shall you make in yourselves any figures or marks: I am the Lord.
29 “‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
Make not thy daughter a common strumpet, lest the land be defiled, and filled with wickedness.
30 “‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
Keep ye my sabbaths, and reverence my sanctuary. I am the Lord.
31 “‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Go not aside after wizards, neither ask any thing of soothsayers, to be defiled by them: I am the Lord your God.
32 “‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Rise up before the hoary head, and honour the person of the aged man: and fear the Lord thy God. I am the Lord.
33 “‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
If a stranger dwell in your land, and abide among you, do not upbraid him:
34 Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
But let him be among you as one of the same country: and you shall love him as yourselves: for you were strangers in the land of Egypt. I am the Lord your God.
35 “‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
Do not any unjust thing in judgment, in rule, in weight, or in measure.
36 Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
Let the balance be just and the weights equal, the bushel just, and the sextary equal. I am the Lord your God, that brought you out of the land of Egypt.
37 “‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”
Keep all my precepts, and all my judgments, and do them. I am the Lord.

< Firistoci 19 >