< Firistoci 19 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
HERREN talede fremdeles til Moses og sagde:
2 “Yi wa taron jama’ar Isra’ila gaba ɗaya magana, ka ce musu, ‘Ku zama masu tsarki, domin Ni, Ubangiji Allahnku, mai tsarki ne.
Tal til hele Israeliternes Menighed og sig til dem: I skal være hellige, thi jeg HERREN eders Gud er hellig!
3 “‘Dole kowannenku yă girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, dole kuma ku kiyaye Asabbacina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
I skal frygte hver sin Moder og sin Fader, og mine Sabbater skal I holde. Jeg er HERREN eders Gud!
4 “‘Kada ku juyo ga gumaka, ko ku yi wa kanku allolin da aka yi zubi da ƙarfe. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Vend eder ikke til Afguderne og gør eder ikke støbte Gudebilleder! Jeg er HERREN eders Gud!
5 “‘Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta yadda za tă karɓu a madadinku.
Naar I ofrer Takoffer til HERREN, skal I ofre det saaledes, at I kan vinde Guds Velbehag.
6 Za a ci ta a ranar da kuka miƙa ta, ko kuwa a kashegarin; duk abin da ya rage har kwana ta uku dole a ƙone shi.
Den Dag, I ofrer det, og Dagen efter maa det spises, men hvad der levnes til den tredje Dag, skal opbrændes;
7 In aka ci ta a rana ta uku, marar tsabta ce, ba kuma za a karɓe ta ba.
spises det den tredje Dag, er det at regne for raaddent Kød og vinder ikke Guds Velbehag;
8 Duk wanda ya ci ta zai zama da laifi domin ya ƙazantar da abin da yake da tsarki ga Ubangiji, dole a raba mutumin nan da mutanensa.
den, der spiser deraf, skal undgælde for sin Brøde, thi han vanhelliger det, som var helliget HERREN, og det Menneske skal udryddes af sin Slægt.
9 “‘Sa’ad da kuka yi girbin amfanin gonarku, kada ku girbe har zuwa gefen gonar, ko ku yi kalan girbinku.
Naar I høster eders Lands Høst, maa du ikke høste helt hen til Kanten af din Mark, ej heller maa du sanke Efterslætten efter din Høst.
10 Kada ku koma gonar inabinku kuna kala, ko ku tattara’ya’yan inabin da suka fāffāɗi. Ku bar su domin matalauta da kuma baƙi. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Heller ikke maa du holde Efterhøst eller sanke de nedfaldne Bær i din Vingaard; til den fattige og den fremmede skal du lade det blive tilbage. Jeg er HERREN eders Gud!
11 “‘Kada ku yi sata. “‘Kada ku yi ƙarya. “‘Kada ku ruɗe juna.
I maa ikke stjæle, I maa ikke lyve, I maa ikke bedrage hverandre.
12 “‘Kada ku rantse bisa ƙarya da sunana, ta haka har ku ƙasƙantar da sunan Allahnku. Ni ne Ubangiji.
I maa ikke sværge falsk ved mit Navn, saa du vanhelliger din Guds Navn. Jeg er HERREN!
13 “‘Kada ku zalunci maƙwabcinku, ko ku yi masa ƙwace. “‘Kada ku riƙe albashin ma’aikaci yă kwana.
Du maa intet aftvinge din Næste, du maa intet røve; Daglejerens Løn maa ikke blive hos dig Natten over.
14 “‘Kada ku zagi kurma, ko ku sa abin tuntuɓe a gaban makaho, amma ku ji tsoron Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Du maa ikke forbande den døve eller lægge Stød for den blindes Fod, du skal frygte din Gud. Jeg er HERREN!
15 “‘Kada ku yi rashin adalci cikin shari’a; kada ku nuna sonkai ga matalauci, ko ku goyi bayan mai arziki, amma ku shari’anta maƙwabci cikin gaskiya.
I maa ikke øve Uret, naar I holder Rettergang; du maa ikke begunstige den ringe, ej heller tage Parti for den store, men du skal dømme din Næste med Retfærdighed.
16 “‘Kada ku yi ta yawo kuna yaɗa ƙarya a cikin mutanenku. “‘Kada ku yi wani abin da zai sa ran maƙwabcinku cikin hatsari. Ni ne Ubangiji.
Du maa ikke gaa rundt og bagvaske din Landsmand eller staa din Næste efter Livet. Jeg er HERREN!
17 “‘Kada ka yi ƙiyayyar ɗan’uwanka a zuciya. Ka tsawata wa maƙwabcinka da gaske don kada ka sami rabo cikin laifinsa.
Du maa ikke bære Nag til din Broder i dit Hjerte, men du skal tale din Næste til Rette, at du ikke skal paadrage dig Synd for hans Skyld.
18 “‘Kada ka nemi yin ramuwa, ko ka riƙe wani cikin mutanenka a zuciya, amma ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka. Ni ne Ubangiji.
Du maa ikke hævne dig eller gemme paa Vrede mod dit Folks Børn, du skal elske din Næste som dig selv. Jeg er HERREN!
19 “‘Ku kiyaye farillaina. “‘Kada ku sa dabbobin da ba iri ɗaya ba su yi barbara. “‘Kada ku yi shuki iri biyu a gonarku. “‘Kada ku sa rigar da aka saƙa da yadi iri biyu.
Hold mine Anordninger! Du maa ikke lade to Slags Kvæg parre sig med hinanden; du maa ikke saa to Slags Sæd i din Mark; og du maa ikke bære Klæder, der er vævede af to Slags Garn.
20 “‘In wani ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda aka yi wa wani alkawari amma bai fanshe ta ba, ko kuwa ba a’yantar da ita ba, dole a yi hukuncin da ya dace. Duk da haka ba za a kashe su ba, domin ba a’yantar da ita ba.
Naar en Mand har Samleje med en Kvinde, og det er en Trælkvinde, en anden Mands Medhustru, som ikke er løskøbt eller frigivet, saa skal Afstraffelse finde Sted; dog skal de ikke lide Døden, thi hun var ikke frigivet.
21 Dole mutumin da ya kwana da ita yă kawo rago a ƙofar Tentin Sujada domin hadaya don laifi ga Ubangiji.
Og han skal bringe sit Skyldoffer for HERREN til Aabenbaringsteltets Indgang, en Skyldoffervæder,
22 Da ragon hadaya don laifin ne firist zai yi kafara saboda mutumin a gaban Ubangiji saboda zunubin da ya yi, za a kuwa gafarta zunubinsa.
og Præsten skal med Skyldoffervæderen skaffe ham Soning for HERRENS Aasyn for den Synd, han har begaaet, saa han finder Tilgivelse for den Synd, han har begaaet.
23 “‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar kuka kuma shuka kowane irin itace mai’ya’ya na ci, ku ɗauki’ya’yan itatuwan nan a matsayi an hana ku ci. Shekara uku za ku ɗauka a matsayi an hana ku, ba za ku ci su ba.
Naar I kommer ind i Landet og planter alskens Frugttræer, skal I lade deres Forhud, den første Frugt, urørt; i tre Aar skal de være eder uomskaarne og maa ikke spises;
24 A shekara ta huɗu, dukan’ya’yansu za su zama tsarkakakku, hadaya ta yabo ga Ubangiji.
det fjerde Aar skal al deres Frugt under Høstjubel helliges HERREN;
25 Amma a shekara ta biyar, za ku iya cin’ya’yan itatuwan. Ta haka girbinku zai ƙaru. Ni ne Ubangiji Allahnku.
først det femte Aar maa I spise deres Frugt, for at I kan faa saa meget større Udbytte deraf. Jeg er HERREN eders Gud!
26 “‘Kada ku ci wani abinci tare da jini a cikinsa. “‘Kada ku yi duba ko sihiri.
I maa ikke spise noget med Blodet i. I maa ikke give eder af med at tage Varsler og øve Trolddom.
27 “‘Ba za ka aske gefe-gefe na gashin kanka ba, ko ku aske gemunku.
I maa ikke runde Haaret paa Tindingerne; og du maa ikke studse dit Skæg;
28 “‘Kada ku tsattsaga jikunanku saboda matattu, ba kuwa za ku yi wa kanku zāne-zāne a jiki ba. Ni ne Ubangiji.
I maa ikke gøre Indsnit i eders Legeme for de dødes Skyld eller indridse Tegn paa eder. Jeg er HERREN!
29 “‘Kada ka ƙasƙantar da’yarka ta wurin mai da ita karuwa, in ba haka ba ƙasar za tă juya ga karuwanci tă kuma cika da mugunta.
Du maa ikke vanhellige din Datter ved at lade hende bedrive Hor, for at ikke Landet skal forfalde til Horeri og fyldes med Utugt.
30 “‘Ku kiyaye Asabbacina, ku kuma girmama wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji.
Mine Sabbater skal I holde, og min Helligdom skal I frygte. Jeg er HERREN!
31 “‘Kada ku juya ga masu duba, ko ku nemi shawarar bokaye, gama za ku ƙazantu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Henvend eder ikke til Genfærd og Sandsigeraander; søg dem ikke, saa I gør eder urene ved dem. Jeg er HERREN eders Gud!
32 “‘Ku miƙe tsaye a gaban tsofaffi, ku nuna bangirma ga waɗanda suka tsufa, ku kuma girmama Allahnku. Ni ne Ubangiji.
Du skal rejse dig for de graa Haar og ære Oldingen, og du skal frygte din Gud. Jeg er HERREN!
33 “‘Sa’ad da baƙo yana zama tare da ku a ƙasarku, kada ku wulaƙanta shi.
Naar en fremmed bor hos dig i eders Land, maa I ikke lade ham lide Overlast;
34 Dole ku ɗauki baƙon da yake zama tare da ku kamar haifaffe ɗan ƙasa. Ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.
som en af eders egne skal I regne den fremmede, der bor hos eder, og du skal elske ham som dig selv, thi I var selv fremmede i Ægypten. Jeg et HERREN eders Guld!
35 “‘Kada ku yi amfani da mudun ƙarya sa’ad da kuke awon tsawo, nauyi, ko yawan abu.
Naar I holder Rettergang, maa I ikke øve Uret ved Længdemaal, Vægt eller Rummaal;
36 Ku yi amfani da ma’auni na gaskiya da mudu na gaskiya, da kuma magwaji na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar.
Vægtskaale, der vejer rigtigt, Lodder, der holder Vægt, Efa og Hin, der holder Maal, skal I have. Jeg er HERREN eders Gud, som førte eder ud af Ægypten!
37 “‘Ku kiyaye dukan farillaina da kuma dukan dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.’”
Hold alle mine Anordninger og Lovbud og gør efter dem. Jeg er HERREN!

< Firistoci 19 >