< Firistoci 18 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Fallou mais o Senhor a Moysés, dizendo:
2 “Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
Falla aos filhos de Israel, e dize-lhes: Eu sou o Senhor vosso Deus.
3 Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
Não fareis segundo as obras da terra do Egypto, em que habitastes, nem fareis segundo as obras da terra de Canaan, na qual eu vos metto, nem andareis nos seus estatutos.
4 Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Fareis conforme aos meus juizos, e os meus estatutos guardareis, para andardes n'elles: Eu sou o Senhor vosso Deus,
5 Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
Portanto os meus estatutos e os meus juizos guardareis; os quaes, fazendo o homem, viverá por elles: Eu sou o Senhor.
6 “‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
Nenhum homem se chegará a qualquer parenta da sua carne, para descobrir a sua nudez: Eu sou o Senhor.
7 “‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
Não descobrirás a nudez de tua mãe: ella é tua mãe; não descobrirás a sua nudez.
8 “‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
Não descobrirás a nudez da mulher de teu pae.
9 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
A nudez de tua irmã, filha de teu pae, ou filha de tua mãe, nascida em casa, ou fóra da casa, a sua nudez não descobrirás.
10 “‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
A nudez da filha do teu filho, ou da filha de tua filha, a sua nudez não descobrirás: porque ella é tua nudez.
11 “‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
A nudez da filha da mulher de teu pae, gerada de teu pae (ella é tua irmã), a sua nudez não descobrirás.
12 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
A nudez da irmã de teu pae não descobrirás; ella é parenta de teu pae
13 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
A nudez da irmã de tua mãe não descobrirás; pois ella é parenta de tua mãe.
14 “‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
A nudez do irmão de teu pae não descobrirás; não chegarás á sua mulher; ella é tua tia.
15 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
A nudez de tua nora não descobrirás: ella é mulher de teu filho: não descobrirás a sua nudez.
16 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
A nudez da mulher de teu irmão não descobrirás; é a nudez de teu irmão.
17 “‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
A nudez d'uma mulher e de sua filha não descobrirás: não tomarás a filha de seu filho, nem a filha de sua filha, para descobrir a sua nudez; parentas são: maldade é.
18 “‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
E não tomarás uma mulher com sua irmã, para affligil-a, descobrindo a sua nudez com ella na sua vida.
19 “‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
E não chegarás á mulher durante a separação da sua immundicia, para descobrir a sua nudez,
20 “‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
Nem te deitarás com a mulher de teu proximo para copula de semente, para te contaminar com ella.
21 “‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
E da tua semente não darás para fazer passar pelo fogo perante Molech; e não profanarás o nome de teu Deus: Eu sou o Senhor.
22 “‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
Com macho te não deitarás, como se fosse mulher: abominação é;
23 “‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
Nem te deitarás com um animal, para te não contaminar com elle: nem a mulher se porá perante um animal, para ajuntar-se com elle; confusão é.
24 “‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
Com nenhuma d'estas coisas vos contamineis: porque em todas estas coisas se contaminaram as gentes que eu lanço fóra de diante da vossa face.
25 Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
Pelo que a terra está contaminada; e eu visitarei sobre ella a sua iniquidade, e a terra vomitará os seus moradores.
26 Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
Porém vós guardareis os meus estatutos e os meus juizos, e nenhuma d'estas abominações fareis, nem o natural, nem o estrangeiro que peregrina entre vós
27 gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
Porque todas estas abominações fizeram os homens d'esta terra, que n'ella estavam antes de vós; e a terra foi contaminada.
28 Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
Para que a terra vos não vomite, havendo-a contaminado, como vomitou a gente que n'ella estava antes de vós.
29 “‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
Porém, qualquer que fizer alguma d'estas abominações, as almas que as fizeram serão extirpadas do seu povo.
30 Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Portanto guardareis o meu mandado, não fazendo nenhum dos estatutos abominaveis que se fizeram antes de vós, e não vos contamineis com elles: Eu sou o Senhor vosso Deus.