< Firistoci 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
L'Éternel parla aussi à Moïse, en disant:
2 “Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
Parle aux enfants d'Israël, et dis-leur: Je suis l'Éternel, votre Dieu.
3 Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
Vous ne ferez point ce qui se fait dans le pays d'Égypte, où vous avez habité, ni ce qui se fait au pays de Canaan où je vous mène: vous ne marcherez point selon leurs lois.
4 Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
Vous pratiquerez mes ordonnances, et vous garderez mes lois pour les suivre: Je suis l'Éternel, votre Dieu.
5 Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
Vous garderez donc mes lois et mes ordonnances; l'homme qui les pratiquera vivra par elles: Je suis l'Éternel.
6 “‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
Nul de vous ne s'approchera de sa proche parente, pour découvrir sa nudité: Je suis l'Éternel.
7 “‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
Tu ne découvriras point la nudité de ton père, ni la nudité de ta mère; c'est ta mère: tu ne découvriras point sa nudité.
8 “‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
Tu ne découvriras point la nudité de la femme de ton père; c'est la nudité de ton père.
9 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
Tu ne découvriras point la nudité de ta sœur, fille de ton père ou fille de ta mère, née dans la maison ou née hors de la maison.
10 “‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
Tu ne découvriras point la nudité de la fille de ton fils ou de la fille de ta fille, car c'est ta nudité.
11 “‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
Tu ne découvriras point la nudité de la fille de la femme de ton père, née de ton père; c'est ta sœur.
12 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
Tu ne découvriras point la nudité de la sœur de ton père; elle est la chair de ton père.
13 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
Tu ne découvriras point la nudité de la sœur de ta mère; car elle est la chair de ta mère.
14 “‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
Tu ne découvriras point la nudité du frère de ton père, tu ne t'approcheras point de sa femme; c'est ta tante.
15 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
Tu ne découvriras point la nudité de ta belle-fille; c'est la femme de ton fils; tu ne découvriras point sa nudité.
16 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
Tu ne découvriras point la nudité de la femme de ton frère; c'est la nudité de ton frère.
17 “‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
Tu ne découvriras point la nudité d'une femme et de sa fille; tu ne prendras point la fille de son fils, ni la fille de sa fille, pour découvrir leur nudité; elles sont tes proches parentes; c'est un crime.
18 “‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
Tu ne prendras point une femme avec sa sœur, pour exciter une rivalité, en découvrant sa nudité à côté de ta femme pendant sa vie.
19 “‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
Tu ne t'approcheras pas d'une femme pendant son impureté pour découvrir sa nudité.
20 “‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
Tu n'auras point commerce avec la femme de ton prochain, pour te souiller avec elle.
21 “‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
Tu ne donneras point de tes enfants pour les faire passer par le feu à Moloc; et tu ne profaneras point le nom de ton Dieu: Je suis l'Éternel.
22 “‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
Tu ne coucheras point avec un homme, comme on couche avec une femme; c'est une abomination.
23 “‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
Tu n'auras commerce avec aucune bête pour te souiller avec elle; une femme ne se prostituera point à une bête; c'est une abomination.
24 “‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
Ne vous souillez par aucune de ces choses; car c'est par toutes ces choses que se sont souillées les nations que je vais chasser de devant vous.
25 Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
La terre en a été souillée; et je punirai sur elle son iniquité, et la terre vomira ses habitants.
26 Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
Mais vous, vous garderez mes lois et mes ordonnances, et vous ne ferez aucune de ces abominations, ni celui qui est né au pays, ni l'étranger qui séjourne au milieu de vous.
27 gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
Car toutes ces abominations, les hommes du pays, qui y ont été avant vous, les ont faites et la terre en a été souillée.
28 Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
Et la terre ne vous vomira pas, pour l'avoir souillée, comme elle a vomi la nation qui y était avant vous.
29 “‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
Car tous ceux qui feront quelqu'une de toutes ces abominations, seront retranchés du milieu de leur peuple.
30 Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Vous observerez donc ce que j'ordonne, afin de ne pratiquer aucune des coutumes abominables qui ont été pratiquées avant vous, et vous ne vous souillerez point par elles. Je suis l'Éternel, votre Dieu.

< Firistoci 18 >