< Firistoci 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said to Moses/me,
2 “Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
“Speak to the Israeli people and tell them [that I, Yahweh, say this] this: I am Yahweh, your God.
3 Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
[So you must do what I want you to do]; you must not do the things that the people in Egypt, where you lived previously, do; and you must not do what is done by the people in Canaan, the land to which I am taking you. Do not imitate their behavior.
4 Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
You must obey all of my laws [DOU], because it is I, Yahweh your God, [who am commanding those laws].
5 Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
If you obey all my laws and decrees, you will continue to remain alive [for a long time]. I, Yahweh, [am the one who is promising that to you]. [These are some of my laws]:
6 “‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
“Do not have sex with any of your close relatives. It is I, Yahweh, [who am commanding that].
7 “‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
“Do not disgrace your father by having sex with your mother [DOU].
8 “‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
“Do not have sex with any of your father’s [other] wives, because that would disgrace your father.
9 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
“Do not have sex with your sister or your stepsister; it does not matter whether she was born in your house or somewhere else.
10 “‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
“Do not have sex with your granddaughter, because that would disgrace you.
11 “‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
“Do not have sex with your half-sister, because she is your sister.
12 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
“Do not have sex with your father’s sister, because she is your father’s close relative.
13 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
“Do not have sex with your mother’s sister, because she is your mother’s close relative.
14 “‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
“Do not disgrace your (uncle/father’s brother) by having sex with his wife, because she is your aunt.
15 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
“Do not have sex with [DOU] your daughter-in-law, because she is your son’s wife.
16 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
“Do not have sex with your brother’s wife, because that would disgrace your brother.
17 “‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
“Do not have sex with the daughter or granddaughter of any woman whom you have previously had sex with; they are [her] (OR, [your]) close relatives. Having sex with any of them would be a wicked thing to do.
18 “‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
“While your wife is still living, do not marry your wife’s sister and have sex with her.
19 “‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
“Do not have sex with any woman while she is having her monthly menstrual period.
20 “‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
“Do not (defile yourself/make yourself unacceptable to me) by having sex with someone else’s wife.
21 “‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
“Do not give any of your children to be burned to be a sacrifice to the god Molech, because that would show that you do not revere me [MTY], Yahweh, your God.
22 “‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
“No man should have sex with another man; that is detestable.
23 “‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
“No one, man or woman, should (defile himself/cause himself to become unacceptable to me) by having sex with an animal; that is a perverse act.
24 “‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
“Do not (defile yourselves/cause yourselves to become unacceptable to me) in any of those ways, because doing those things is how the people of the nations that I expelled as you advanced became (unacceptable to me/defiled).
25 Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
They even caused the land to become defiled, so I punished them for their sins, and [it was as though] the land vomited out the people who lived there.
26 Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
You must all obey my laws and decrees. That includes you people who were born here and the foreigners who live among you.
27 gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
All those detestable things were done by the people who lived in this land before you came here, and they caused the land to become defiled.
28 Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
So if you defile the land, I will get rid of [MET] you like I got rid of the people of those nations that were here before you came.
29 “‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
“You must not allow people who do any of those detestable things to associate with you who are my people.
30 Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Obey everything that I command you to do, and do not defile yourselves by practicing any of the detestable customs that were practiced [by the people who were there] before you came. I, Yahweh your God, [am the one who is commanding these things].”

< Firistoci 18 >