< Firistoci 18 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke to Moses, saying,
2 “Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
Speak to the children of Israel, and say to them, I am the LORD your God.
3 Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
After the doings of the land of Egypt, wherein you dwelled, shall you not do: and after the doings of the land of Canaan, where I bring you, shall you not do: neither shall you walk in their ordinances.
4 Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
You shall do my judgments, and keep my ordinances, to walk therein: I am the LORD your God.
5 Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
You shall therefore keep my statutes, and my judgments: which if a man do, he shall live in them: I am the LORD.
6 “‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
None of you shall approach to any that is near of kin to him, to uncover their nakedness: I am the LORD.
7 “‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
The nakedness of your father, or the nakedness of your mother, shall you not uncover: she is your mother; you shall not uncover her nakedness.
8 “‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
The nakedness of your father’s wife shall you not uncover: it is your father’s nakedness.
9 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
The nakedness of your sister, the daughter of your father, or daughter of your mother, whether she be born at home, or born abroad, even their nakedness you shall not uncover.
10 “‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
The nakedness of your son’s daughter, or of your daughter’s daughter, even their nakedness you shall not uncover: for theirs is your own nakedness.
11 “‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
The nakedness of your father’s wife’s daughter, begotten of your father, she is your sister, you shall not uncover her nakedness.
12 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
You shall not uncover the nakedness of your father’s sister: she is your father’s near kinswoman.
13 “‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
You shall not uncover the nakedness of your mother’s sister: for she is your mother’s near kinswoman.
14 “‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
You shall not uncover the nakedness of your father’s brother, you shall not approach to his wife: she is your aunt.
15 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
You shall not uncover the nakedness of your daughter in law: she is your son’s wife; you shall not uncover her nakedness.
16 “‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
You shall not uncover the nakedness of your brother’s wife: it is your brother’s nakedness.
17 “‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
You shall not uncover the nakedness of a woman and her daughter, neither shall you take her son’s daughter, or her daughter’s daughter, to uncover her nakedness; for they are her near kinswomen: it is wickedness.
18 “‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
Neither shall you take a wife to her sister, to vex her, to uncover her nakedness, beside the other in her life time.
19 “‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
Also you shall not approach to a woman to uncover her nakedness, as long as she is put apart for her uncleanness.
20 “‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
Moreover you shall not lie carnally with your neighbor’s wife, to defile yourself with her.
21 “‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
And you shall not let any of your seed pass through the fire to Molech, neither shall you profane the name of your God: I am the LORD.
22 “‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
You shall not lie with mankind, as with womankind: it is abomination.
23 “‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
Neither shall you lie with any beast to defile yourself therewith: neither shall any woman stand before a beast to lie down thereto: it is confusion.
24 “‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
Defile not you yourselves in any of these things: for in all these the nations are defiled which I cast out before you:
25 Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
And the land is defiled: therefore I do visit the iniquity thereof on it, and the land itself vomits out her inhabitants.
26 Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
You shall therefore keep my statutes and my judgments, and shall not commit any of these abominations; neither any of your own nation, nor any stranger that sojourns among you:
27 gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
(For all these abominations have the men of the land done, which were before you, and the land is defiled; )
28 Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
That the land spew not you out also, when you defile it, as it spewed out the nations that were before you.
29 “‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
For whoever shall commit any of these abominations, even the souls that commit them shall be cut off from among their people.
30 Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
Therefore shall you keep my ordinance, that you commit not any one of these abominable customs, which were committed before you, and that you defile not yourselves therein: I am the LORD your God.

< Firistoci 18 >