< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Fallou mais o Senhor a Moysés, dizendo:
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Falla a Aarão e aos seus filhos, e a todos os filhos d'Israel, e dize-lhes: Esta é a palavra que o Senhor ordenou, dizendo:
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
Qualquer homem da casa de Israel que degolar boi, ou cordeiro, ou cabra, no arraial, ou quem os degolar fóra do arraial,
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
E os não trouxer á porta da tenda da congregação, para offerecer offerta ao Senhor diante do tabernaculo do Senhor, a tal homem será imputado o sangue; derramou sangue: pelo que tal homem será extirpado do seu povo,
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
Para que os filhos de Israel, trazendo os seus sacrificios, que sacrificam sobre a face do campo, os tragam ao Senhor, á porta da tenda da congregação, ao sacerdote, e os sacrifiquem por sacrificios pacificos ao Senhor.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
E o sacerdote espargirá o sangue sobre o altar do Senhor, á porta da tenda da congregação, e queimará a gordura por cheiro suave ao Senhor.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
E nunca mais sacrificarão os seus sacrificios aos demonios, após os quaes elles fornicam: isto ser-lhes-ha por estatuto perpetuo nas suas gerações.
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
Dize-lhes pois: Qualquer homem da casa de Israel, ou dos estrangeiros que peregrinam entre vós, que offerecer holocausto ou sacrificio,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
E não trouxer á porta da tenda da congregação, para offerecel-o ao Senhor, o tal homem será extirpado dos seus povos.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
E, qualquer homem da casa de Israel, ou dos estrangeiros que peregrinam entre elles, que comer algum sangue, contra aquella alma que comer sangue, eu porei a minha face, e a extirparei do seu povo.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
Porque a alma da carne está no sangue; pelo que vol o tenho dado sobre o altar, para fazer expiação pelas vossas almas: porquanto é o sangue que fará expiação pela alma.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
Portanto tenho dito aos filhos de Israel: Nenhuma alma de entre vós comerá sangue, nem o estrangeiro, que peregrine entre vós, comerá sangue.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
Tambem, qualquer homem dos filhos de Israel, ou dos estrangeiros que peregrinam entre elles, que caçar caça d'animal ou d'ave que se come, derramará o seu sangue, e o cobrirá com pó;
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
Porquanto é a alma de toda a carne; o seu sangue é pela sua alma: por isso tenho dito aos filhos de Israel: Não comereis o sangue de nenhuma carne, porque a alma de toda a carne é o seu sangue; qualquer que o comer será extirpado.
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
E toda a alma entre os naturaes, ou entre os estrangeiros, que comer corpo morto ou dilacerado, lavará os seus vestidos, e se banhará com agua, e será immunda até á tarde; depois será limpa
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
Mas, se os não lavar, nem banhar a sua carne, levará sobre si a sua iniquidade.

< Firistoci 17 >