< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Parle à Aaron et à ses fils et à tous les enfants d’Israël, leur disant: Voici la parole qu’a commandée le Seigneur, disant:
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
Un homme, quel qu’il soit de la maison d’Israël, s’il a tué un bœuf, ou une brebis, ou une chèvre, dans le camp, ou hors du camp,
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
Et qu’il ne l’ait pas présentée à la porte du tabernacle comme oblation au Seigneur, sera coupable de sang: comme s’il avait répandu le sang, ainsi il périra du milieu de son peuple.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
À cause de cela les enfants d’Israël doivent présenter au prêtre leurs hosties qu’ils tueront dans la campagne, afin qu’elles soient consacrées au Seigneur devant la porte du tabernacle de témoignage, et qu’ils les immolent comme des hosties pacifiques au Seigneur.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
Et le prêtre répandra le sang sur l’autel du Seigneur à la porte du tabernacle de témoignage, et il brûlera la graisse en odeur de suavité pour le Seigneur.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
Ainsi ils n’immoleront jamais plus leurs hosties aux démons, avec lesquels ils ont forniqué. Ce sera une loi perpétuelle pour eux et pour leurs descendants.
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
Et tu leur diras à eux-mêmes: Un homme de la maison d’Israël, et d’entre les étrangers qui séjournent chez vous, qui aura offert un holocauste ou une victime,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
Et ne l’amènera pas à la porte du tabernacle de témoignage, pour qu’elle soit offerte au Seigneur, périra du milieu de son peuple.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
Un homme, quel qu’il soit de la maison d’Israël, et d’entre les étrangers qui séjournent parmi eux, s’il mange du sang, j’affermirai ma face contre son âme, et je l’exterminerai du milieu de son peuple,
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
Parce que lame de la chair est dans le sang; or, c’est moi qui vous l’ai donné, afin qu’avec lui vous fassiez sur l’autel des expiations pour vos âmes, et que le sang serve ainsi à l’expiation de l’âme.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
C’est pourquoi j’ai dit aux enfants d’Israël: Nul d’entre vous ne mangera du sang, ni aucun d’entre les étrangers qui séjournent chez vous.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
Un homme quelconque d’entre les enfants d’Israël et d’entre les étrangers, qui séjournent chez vous, s’il prend à la chasse et au filet une bête sauvage ou un oiseau, dont il est permis de manger, qu’il répande son sang et le couvre de terre.
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
Car l’âme de toute chair est dans le sang; c’est pourquoi j’ai dit aux enfants d’Israël: Vous ne mangerez le sang d’aucune chair, parce que l’âme de la chair est dans le sang: et quiconque en mangera, périra.
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
Un homme, tant d’entre les indigènes que d’entre les étrangers, qui mangera d’un animal crevé, ou pris par une bête sauvage, lavera ses vêtements et soi-même dans l’eau, et il sera souillé jusqu’au soir: et c’est de cette manière qu’il deviendra pur.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
Que s’il ne lave pas ses vêtements et son corps, il portera son iniquité.

< Firistoci 17 >