< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Parle à Aaron, à ses fils et à tous les enfants d'Israël, et tu leur diras: « Voici ce que Yahvé a ordonné:
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
Tout homme de la maison d'Israël qui aura tué un taureau, un agneau ou une chèvre dans le camp, ou qui l'aura tué hors du camp,
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
et qui ne l'aura pas apporté à l'entrée de la tente d'assignation pour l'offrir en sacrifice à l'Éternel devant la tente de l'Éternel: le sang sera imputé à cet homme. Il a versé le sang. Cet homme sera retranché du milieu de son peuple.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
Ceci afin que les enfants d'Israël apportent leurs sacrifices, qu'ils sacrifient en plein champ, afin qu'ils les apportent à l'Éternel, à l'entrée de la tente d'assignation, au sacrificateur, et qu'ils les offrent en sacrifice d'actions de grâces à l'Éternel.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
Le prêtre aspergera le sang sur l'autel de l'Éternel, à l'entrée de la Tente d'assignation, et il brûlera la graisse en parfum d'agrément pour l'Éternel.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
Ils n'offriront plus leurs sacrifices aux idoles de boucs, après lesquelles ils se prostituent. Ce sera pour eux une loi à perpétuité, de génération en génération ».
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
« Tu leur diras: « Tout homme de la maison d'Israël ou des étrangers qui vivent au milieu d'eux, qui offre un holocauste ou un sacrifice,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
et qui ne l'apporte pas à l'entrée de la tente de la Rencontre pour le sacrifier à Yahvé, cet homme sera retranché de son peuple.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
"'Tout homme de la maison d'Israël, ou des étrangers qui vivent au milieu d'eux, qui mange du sang, quel qu'il soit, je tournerai ma face contre cet homme qui mange du sang, et je le retrancherai du milieu de son peuple.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
Car la vie de la chair est dans le sang. Je vous l'ai donné sur l'autel pour faire l'expiation de vos âmes, car c'est le sang qui fait l'expiation à cause de la vie.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
C'est pourquoi j'ai dit aux enfants d'Israël: « Personne parmi vous ne pourra manger du sang, et aucun étranger vivant au milieu de vous ne pourra manger du sang. »
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
"'Tout homme des enfants d'Israël ou des étrangers qui vivent au milieu d'eux, qui prendra à la chasse un animal ou un oiseau comestible, en versera le sang et le couvrira de poussière.
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
Car pour ce qui est de la vie de toute chair, son sang est avec sa vie. C'est pourquoi j'ai dit aux enfants d'Israël: « Vous ne mangerez pas le sang d'aucune espèce de chair, car la vie de toute chair, c'est son sang. Celui qui en mangera sera retranché. »
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
"'Toute personne qui mangera ce qui meurt d'elle-même ou ce qui est déchiré par les animaux, qu'elle soit native ou étrangère, lavera ses vêtements, se baignera dans l'eau et sera impure jusqu'au soir. Ensuite, il sera pur.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
Mais s'il ne les lave pas et ne se lave pas, il portera la peine de son iniquité.'"

< Firistoci 17 >