< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh also said to Moses/me,
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
“Speak to Aaron and his sons and to all the other Israeli people, and say this to them: ‘This is what Yahweh has commanded:
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
If you sacrifice an ox or a lamb or a goat, you must bring it [to the priest] at the entrance of the Sacred Tent [area], to present/offer it to me there.
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
If you slaughter it to be a sacrifice anywhere else in the camp or outside the camp, you will be guilty of killing an animal [in an unacceptable place]. As a result you will no longer be allowed to be/associate with my people.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
That rule is in order that you Israeli people, instead of offering sacrifices in the open fields, will offer them to me by taking them to the priest at the entrance of the Sacred Tent [area], to be offerings to maintain fellowship [with me].
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
[After the animal is slaughtered], the priest must sprinkle some of its blood against the altar at the entrance of the Sacred Tent, and burn its fat to be an aroma that is pleasing to me.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
You people must no longer give sacrifices to the demons that resemble goats which you are worshiping. You people must obey this command forever.’
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
“And tell this to the people: ‘If any Israeli or any foreigner who is living among them brings an offering that is to be completely burned [on the altar], or any other sacrifice,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
and does not bring it to the entrance of the Sacred Tent [area] to be a sacrifice to me, that person will no longer be allowed to associate with my people.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
‘I will reject [IDM] any Israeli or any foreigner who is living among you who eats any blood, and I [will command that he] no longer be allowed to associate with my people.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
That is because the life of every creature is in its blood; I have declared that it is blood that is to be offered on the altar to enable people to be forgiven for their sins.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
That is why I say that you Israelis must not eat blood, and the foreigners who live among you must also not eat blood.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
‘Any Israeli or any foreigner who is living among you who hunts any animal or bird that is permitted for you to eat, must drain out the blood [of the animal or bird that he kills], and cover the blood with dirt.
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
This is because the life of every creature is in its blood. And that is why I have said [DOU] to you Israelis that anyone who eats blood must no longer [be allowed to associate with my people].
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
‘Anyone in Israel, including foreigners, who eats any of the meat of any creature that is found dead, or that had been killed by wild animals, must wash his clothes and bathe. Then he must not touch anyone until that evening.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
If he does not do those things, he will be punished for what he did.’”

< Firistoci 17 >