< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke unto Moses, saying,
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Speak unto Aaron, and unto his sons, and unto all the children of Israel, and say unto them, This is the thing which the Lord hath commanded, saying,
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
Any man whatsoever of the house of Israel, that killeth an ox, or a sheep, or a goat, in the camp, or that killeth it out of the camp,
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
And bringeth it not to the door of the tabernacle of the congregation, to offer it as an offering unto the Lord before the tabernacle of the Lord: as blood-guiltiness shall it be imputed unto that man, blood hath he shed; and that man shall be cut off from among his people.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
In order that the children of Israel may bring their sacrifices, which they slay in the open field, and bring them unto the Lord, to the door of the tabernacle of the congregation, unto the priest, and slay them as sacrifices of peace-offerings unto the Lord.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
And the priest shall sprinkle the blood upon the altar of the Lord at the door of the tabernacle of the congregation; and he shall burn the fat for a sweet savor unto the Lord.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
So that they shall offer no more their sacrifices unto evil spirits, after which they have gone astray: a statute for ever shall this be unto them throughout their generations.
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
And unto them shalt thou say, Whatsoever man there be of the house of Israel, or of the strangers who may sojourn among them, that offereth a burnt-offering or a sacrifice,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
And bringeth it not unto the door of the tabernacle of the congregation, to offer it unto the Lord: even that man shall be cut off from among his people.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
And if there be any man of the house of Israel, or of the strangers that sojourn among them, that eateth any manner of blood: I will set my face against the person that eateth the blood, and I will cut him off from among his people.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
For the life of the flesh is in the blood; and I have appointed it for you upon the altar to make an atonement for your souls; for the blood it is that maketh an atonement for the soul.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
Therefore have I said unto the children of Israel, No one of you shall eat blood, and the stranger that sojourneth among you shall not eat blood.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
And if there be any man whatsoever of the children of Israel, or of the strangers that sojourn among them, who catcheth by hunting any beast or fowl that may be eaten: then shall he pour out the blood thereof, and cover it up with dust.
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
For the life of all flesh is its blood, on which its life dependeth; therefore have I said unto the children of Israel, The blood of every manner of flesh shall ye not eat; for the life of all flesh is its blood, every one who eateth it shall be cut off.
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
And every person that eateth that which hath died of itself, or that which was torn by beasts, be this one born in your own country, or a stranger, shall both wash his clothes, and bathe himself in water, and be unclean until the evening, when he shall be clean.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
But if he wash [them] not, nor bathe his flesh, then shall he bear his iniquity.

< Firistoci 17 >