< Firistoci 17 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spake vnto Moses, saying,
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
Speake vnto Aaron, and to his sonnes, and to all the children of Israel, and say vnto them, This is the thing which the Lord hath commanded, saying,
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
Whosoeuer he be of the house of Israel that killeth a bullocke, or lambe, or goate in the hoste, or that killeth it out of the hoste,
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
And bringeth it not vnto the doore of the Tabernacle of the Congregation to offer an offring vnto the Lord before the Tabernacle of the Lord, blood shalbe imputed vnto that man: he hath shed blood, wherefore that man shall be cut off from among his people.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
Therefore the children of Israel shall bring their offrings, which they would offer abroad in the fielde, and present the vnto ye Lord at the doore of the Tabernacle of ye Congregation by ye Priest, and offer them for peace offrings vnto the Lord.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
Then the Priest shall sprinkle the blood vpon the Altar of the Lord before the doore of the Tabernacle of the Congregation, and burne the fat for a sweete sauour vnto the Lord.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
And they shall no more offer their offerings vnto deuils, after whom they haue gone a whoring: this shalbe an ordinance for euer vnto them in their generations.
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
Also thou shalt say vnto them, whosoeuer he be of the house of Israel, or of the strangers which soiourne among them, that offreth a burnt offring or sacrifice,
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
And bringeth it not vnto ye doore of the Tabernacle of the Congregation to offer it vnto the Lord, euen that man shall be cut off from his people.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
Likewise whosoeuer he be of the house of Israel, or of the strangers that soiourne among them, that eateth any blood, I will euen set my face against that person that eateth blood, and will cut him off from among his people.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
For the life of the flesh is in the blood, and I haue giuen it vnto you to offer vpon the altar, to make an atonement for your soules: for this blood shall make an atonement for the soule.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
Therefore I saide vnto ye children of Israel, None of you shall eate blood: neither the stranger that soiourneth among you, shall eate blood.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
Moreouer whosoeuer he be of the children of Israel, or of the strangers that soiourne among the, which by hunting taketh any beast or foule that may be eaten, he shall powre out the blood thereof, and couer it with dust:
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
For ye life of all flesh is his blood, it is ioyned with his life: therefore I sayd vnto the children of Israel, Ye shall eate the blood of no flesh: for the life of al flesh is the blood thereof: whosoeuer eateth it, shalbe cut off.
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
And euery person that eateth it which dyeth alone, or that which is torne with beastes, whether it be one of the same countrey or a stranger, he shall both wash his clothes, and wash himselfe in water, and be vncleane vnto the euen: after he shalbe cleane.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
But if he wash them not, nor wash his flesh, then he shall beare his iniquitie.