< Firistoci 16 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
Or, le Seigneur parla à Moïse après la mort des deux fils d’Aaron, quand, offrant un feu étranger, ils furent tués;
2 Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
Et il lui ordonna, disant: Dis à Aaron ton frère, qu’il n’entre pas en tout temps dans le sanctuaire, qui est au dedans du voile devant le propitiatoire dont l’arche est couverte, de peur qu’il ne meure (car j’apparaîtrai dans la nuée sur l’oracle),
3 “Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
S’il ne fait pas auparavant ces choses: il offrira un veau pour le péché et un bélier en holocauste.
4 Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
Il se revêtira d’une tunique de lin, couvrira de caleçons de lin sa nudité; il se ceindra d’une ceinture de lin; il mettra une tiare de lin sur sa tête; car ces vêtements sont saints; il les revêtira tous, lorsqu’il se sera lavé.
5 Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
Il recevra ensuite de la multitude des enfants d’Israël deux boucs pour le péché et un bélier en holocauste.
6 “Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
Et lorsqu’il aura offert le veau, et qu’il aura prié pour lui et pour sa maison,
7 Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
Il présentera les deux boucs devant le Seigneur à la porte du tabernacle de témoignage;
8 Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
Et jetant le sort sur les deux, un sort pour le Seigneur, et l’autre pour le bouc émissaire,
9 Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
Celui dont le sort sera sorti pour le Seigneur, il l’offrira pour le péché;
10 Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
Mais celui dont le sort sera sorti pour le bouc émissaire, il le présentera vivant devant le Seigneur pour répandre des prières sur lui, et l’envoyer dans le désert;
11 “Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
Ces choses faites avec solennité selon les rites, il offrira le veau, et priant pour lui-même et pour sa maison, il l’immolera:
12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
Puis, ayant pris l’encensoir qu’il aura rempli de charbons de l’autel, et prenant de la main le parfum composé pour être brûlé, il entrera au dedans du voile dans les lieux saints;
13 Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
Afin que les parfums étant mis sur le feu, leur fumée et leur vapeur couvre l’oracle, qui est sur le témoignage, et qu’il ne meure point.
14 Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
Il prendra aussi du sang de veau, et il fera l’aspersion avec le doigt sept fois contre le propitiatoire du côté de l’orient,
15 “Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
Et lorsqu’il aura immolé le bouc pour le péché du peuple, il apportera son sang au dedans du voile, comme il a ordonné pour le sang du veau, afin qu’il fasse l’aspersion vis-à-vis de l’oracle,
16 Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
Et qu’il purifie le sanctuaire des impuretés des enfants d’Israël, de leurs prévarications et de tous leurs péchés. Il purifiera selon ce rite le tabernacle de témoignage, qui est dressé parmi eux au milieu des souillures de leur habitation.
17 Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
Que nul homme ne soit dans le tabernacle, quand le pontife entrera dans le sanctuaire, afin de prier pour lui-même et pour sa maison et pour toute l’assemblée d’Israël, jusqu’à ce qu’il sorte.
18 “Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
Mais lorsqu’il sera sorti pour venir à l’autel qui est devant le Seigneur, qu’il prie pour lui-même, et après avoir pris du sang du veau et du bouc, qu’il le répande sur les cornes de l’autel tout autour,
19 Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
Et que faisant l’aspersion avec le doigt sept fois, il le purifie et le sanctifie des impuretés des enfants d’Israël.
20 “Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
Après qu’il aura purifié le sanctuaire, le tabernacle et l’autel, qu’il offre alors le bouc vivant;
21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
Et, les deux mains posées sur sa tête, qu’il confesse toutes les iniquités des enfants d’Israël, tous leurs délits et tous leurs péchés; et les appelant sur sa tête, il l’enverra par un homme choisi pour cela, dans le désert.
22 Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
Et lorsque le bouc aura porté toutes leurs iniquités dans une terre solitaire, et qu’il aura été lâché dans le désert,
23 “Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
Aaron retournera au tabernacle de témoignage, et se dépouillant des vêtements dont il était auparavant revêtu, quand il entrait dans le sanctuaire, et les laissant là,
24 Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
Il lavera sa chair dans un lieu saint, et il se revêtira de ses vêtements. Et après qu’étant sorti, il aura offert son holocauste et celui du peuple, il priera tant pour lui-même que pour le peuple;
25 Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
Et la graisse qui a été offerte pour les péchés, il la brûlera sur l’autel.
26 “Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
Quant à celui qui aura conduit le bouc émissaire, il lavera ses vêtements et son corps dans l’eau, et c’est ainsi qu’il entrera dans le camp.
27 Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
Mais le veau et le bouc qui avaient été immolés pour le péché et dont le sang avait été porté dans le sanctuaire pour que l’expiation fût accomplie, on les emportera hors du camp, et on brûlera au feu, tant leur peau, que leur chair et leur fiente;
28 Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
Et quiconque les aura brûlées, lavera ses vêtements et sa chair dans l’eau, et c’est ainsi qu’il entrera dans le camp.
29 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
Or ceci sera pour vous une loi perpétuelle: Au septième mois, au dixième jour du mois, vous affligerez vos âmes, vous ne ferez aucun travail, soit l’indigène, soit l’étranger qui séjournent parmi vous.
30 gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
En ce jour-là sera votre expiation, et la purification de tous vos péchés; c’est devant le Seigneur que vous serez purifiés;
31 Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
Car c’est un sabbat de repos, et vous affligerez vos âmes par un culte perpétuel.
32 Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
Or il fera la purification, le prêtre qui aura été oint et dont les mains auront été consacrées, pour exercer les fonctions du sacerdoce à la place de son père: et il sera revêtu de la robe de lin et des vêtements saints,
33 yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
Et il purifiera le sanctuaire, le tabernacle de témoignage et l’autel, les prêtres aussi et tout le peuple.
34 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Et ce sera pour vous une loi perpétuelle, que vous priiez pour les enfants d’Israël et pour tous leurs péchés une fois dans l’année. Moïse fit donc comme lui avait ordonné le Seigneur.

< Firistoci 16 >